Tace ƙwarai kuwa, duk wata dukiya ta shamaki ce, sai ta Zeena wadda bata fi cikin cokali ba in aka karata da ta Shamaki."
Nace to kuma kin ci gaba da zama da Zeena ne bayan Hajiya Gwamma ta rasu? Tsohuwa tace 'Ai Shamaki bai rufa wata uku ba ciwo suga ya tasarwa Hajiya Gwamma aka fita da ita ƙasar waje, ashe dai tafiyar kenan.
Sai gawa aka dawo da ita. Zeena ta yi kuka kamar zata yi me har sai da aka yo mata rubutun dangana tasha sannan ta haƙura. Ni kuma da suka gina sabon gida za su tashi sai suka saya mana wannan gidan,a wancan lokacin gida irin wannan sai wane da wane muka dawo. Sai saidai muje muyi aiki lokacin mai gidana ya fara tsufa sai aka kawo sabon direba kuma ta canza wasu masu girki domin nima lokacin girma ya fara shiga kuma ga yara amma dai ina zuwa in yini domin tana son ina zauna kusa da ita kasancewar tana da son labarai. Daga baya kuma sai larurar ido ta kamani, sun kashe min kuɗi amma haka na rasa idanun, sai na hakura da zuwa, Ali Baita shine ya budewa mai gidan nan kati a nan ƙofar gidan muka ci gaba da riƙe kanmu amma Zakka ta fidda kai da ta azumi baya wuce mu har ya rasu Hajiya Zeena bata dai na ba. Sai shekarun nan ne ma aka canza to Gara wannan karon an baku komai da ake bamu.
To kinji."
Nace Lallai Hajiya Zeena ita ma tana da kirki kamar surukar ta.. Tace "Ƙwarai banbanci su kaɗan ne, ita wannan Zeena tana da zafi sosai kuma tana da iko da yawa koda dai mako ance sun shafi sarauta acan garin na su."
Na ce me yasa ake kiran Shamaki da wannan sunan mai makon sunan su na gado wato Aliyu?
.......
*Assalamualaikum*
*Naga addu'o'inku game da sace man waya da akayi, nagode😍*
Tsohuwa Ta ce bani kofin can insha ruwa, ina Maryama ta zo ta kawo muku ruwan kuma."
Jamila ta ce yanzu muka sharuwa . Tsohuwa tace, , "Nima karambani ne 'yannan, nasani gidan Zeena ko masu aiki basa shan ruwa dan awo sai na roba." Ta daga ta sha sosai har ta dan kware, muka tsaya muna yo mata sannu. Tace "Me ki ke tambaya ne? "Nace game da sunan Shamaki.
Ta ce "Anyi haka. Yadda Zeena ta fada min tace Ya samu sunan ne daga asalin mahaifin su acan Sudan Wato shi Baita shine babban yaron sarki kuma duk babban dan sarki to Shamaki ne kuma yana dai dai da Hakimi. Sai Ana ganin shi taro ne bai dace a bashi Shamaki ba. Ya za a ce Sarki yana ji dashi harma ya kasa boye soyayyar sa, har taja aka fara neman rayuwar sa. Sarki ya kira malamai su yi masa istihara akan wannan matsalar,
baki uku ya hadu daga malamai daban daban akan cewa mafi alkhairi shine ya bar garin domin kuwa taurarinsai masu haske suna nesa. Sannan hadari yana kusa da shi.
Haka suka ba Sarki shawara ya nesanta shi daga garin, ya hada shi da amintattu suka kawo shi kasarnan suka juya suka barshi da guzurin shi." todai . Kinji inda ya samo sunan Shamaki. Ali Bauta da Zeena ai suje can kasar a wata shekara.
Kuma sunga dangin su dawo suna yaba karbar da suka samu haka kuma sun zo a rasuwar Ali Baita
Na Kali Jamila nace kinji kuma. Da alamu dai in zamu kwana ba zan daina jin sabbin abubuwa daga bakin tsohuwar nan ba. Tsohuwa tace "Kwarai kuwa. " Nace to wai Kaka Kina gidan Shamaki ya zama saurayi?
Tace "Yana dan makaranta lokacin da na bar gidan ana zancan za a fiddashi kasar waje." Na kada kai, da alamu dai bata da wata masaniya akan Shamaki sosai.
Nace Na gode Kaka dajin Wannan labari na bude jakata na ciro kudi ban kirga ba na kama hannunta na saka mata ina fadin Baba ga su nan a sai miki goro.
Tace "kuma dai ba a gajiya 'yannan Allah ya saka miki da albarka. Kuma naji dadi da wannan ziyara a san da kai ma acrayuwa Ai arziki ne."
Muka fito mukayi musu sallama muka wuce. Muna dansahu na kasa magana ina juya wannan lamari ace wai su Maman Iman ba Uban su daya da Shamaki ba. Jamila tace "Wai in tambaye ki? " Na sauke ajiyar zuciya nace ina jin ki. Tace "Me Wannan labarin zai amfane ki da shi.? "Nace Jamila bazaki gane ba, assignment na ke yi zan hada rahotanni ne tsayo shekara daya. Ta juyo tana kallona alamun bata gane ba. Nace bazaki gane ba. Lokacin da Hajiya Zeena ta juyo da ni zuwa gida da takarda ta ta zaki zaki fi dahimta. Ta zaro ido "Auren shekara daya ku ka yi? " Nace in har shekara ta cika ban san waye Shamaki ba, to zata sa ya sallame ni.
Jamila ta taba baki, wannan gida naku sai kace wani gidan gwamna ko na shugaban kasa."
Nace Ai gidanmu ya wuce nan, domin daga gwamnan har shugaban kasa suna girmama Zeena sun san abinda suke samu daga gareta.
Jamila tace "Wai ma dan ku kuma san hakan Allah ya kyauta."
Da dare Na shirya tsaf Jamila sai tsiya take min wai haka na zama sai wani kakale na ke yi akan miji. Umma ta shigar min tace barta ta yi aikin ladane, ke ai ba a san abinda zaki yi ba.
Bayan ishai sai ga kiran Shamaki wai ga shi a hanya. Dan wani salon da ya zo sai ya tsaya a kofar gida wai in fara fitowa,
Nace ka shigo kai tsaye.
Ya ce fara fitowa mana. Na saka mayafina na fita, yana tsaye a inda ya saba tsaya lokacin da yake zuwa zance. Na gane cewa yana son tuna baya ne, dan haka nima sai naje gurin da nasaba zama na zauna. Nace sannu da zuwa dan samari,. Yace yawwa 'yan mata dazu na ganki ke da wata kanwarki kuma dai na fada sonki irin ta ka dinnan, ya miko tafin hannhu sa, shin ko zaki bani soyayyarki? " Na dora tafin hannu na ina fadin na baka ya kai wannana kyakykkyawan basarake ina fata zaka rike ni amana bazaka sake ni ba.. Ka sani babu wata mace wadda zaka yi mata tayin soyayyarka ta kauda kai. Ina sonka. Sai ya janwo ni jikinsa yana fadin nima ina sonki yake wannan yarinya mai kyau da iya kalami.
Sai duk muka sa dariya ya sake ni tare da fadin muje in gaida su Umma. " Muka nufi cikin gida. Tuni an shinfida masa shinfida, suka gaisa daga nan sai Abba da Umma suka yi masa godiyar sako. Ya ce babu komi ya dada ciro kadi ya aje wa Umma sannan ya aje wa Abbbanmu. Suka sake yin godiya, sannan Abba yace kuje ki raka shi ya gaida Abban su Zuhra kafin ku wuce ko?" Nace to. Muka fita yace mu taka a kafa muje." Abarandar da suke salla muka same shi, shida wasu makotan su. Muka durkusa muka gaida su, yace Uwata ce sannunku muka gaisa ya ciro kudi ya ba Abban su Zuhra, sannan suma na zaune ya ciro ya basu.
Suna ta saka albarka, daga nan muka koma mota, muna shiga ya rungume yana neman bakina, na biye shi na tsawon lokaci kafin daga baya na zame nace atiti muke ya sake kamoni, my Baby mu bivu ne anan ba mai ganinmu. Ya yamutsani son ransa, da kyar na lallabashi. Ya figi mota da gudu. Ni dashi babu wanda ya iya furta wata kalma. Kaina na jingina sa a bayan kujera na lumshe ido kamar mai bacci. Duk ya saukar min kasala, gashi yanzu in munje gida gurin Hajiya zamu yada zango. Shims nasan damuwar kenan.
Koda ya yi hon har aka bude mana gate ban iya dago kaina ba. Sai da ya tsaya ya sa hannu ya shafi wuyana,sannan ya daga wayarsa ya soma magana cikin harshen turanci, duk da banajin sosai kunsan karatunmu na Kano in ba makarantar kudi ka yi ba sai a hankali na tsinci kalma biyu. My wife sai kuma da ya gama maganar naji yace ok. Na tashi da niyyar fita sai na ga ashe ba gida muka zo ba. Nace Babban bako ina ne nan? Yace karanta can ya nuna min wasu rubutu masu kawo wuta. Hotel din ne ya dauki hankali na ba sunan Hotel din ba.
Na dubeshi da sauri, Subahanallahi Auzu billahi minasshaidanin rajim! Me zamuyi a Hotel da mutuncinmu da komai! Me zan gani Shamaki? Yace "Me ake yi kuma me ake gani a Hotel din da zaki gigice haka? "
Nace 'Yan iska ke zuwa Hotel yin iskanci. Yace "Muma iskancin muka zo muyi." Na zaro idanu har zuciyata zunubi ne zuwanmu gurin nan dan haka na bata rai nayi shiru. Ya daga wayar shi sai naji ya sake furta ok. Ya bude mota, fito muje." Na ki motsi ya fita ya zagayo ya bude yace fito mana baby." Na soma zubo hawaye domin take zuciyata take fada min wai inda yake zuwa da matan banzan shi ne. Ya katse ni, ina miki magana kina jina? Da alama ya soma fusata. Cikin kuka, nace yanzu fisabililllahi in wani ya gammu yaje ya fadawa Abbanmu cewa ya ganni a Hotel tsine min zai yi fa. Ya saka hannu ya dakko ni ya rike ni kamar wata jinjira, sannan ya rufe motar ya sabani a kafa yace a haka kinga baby bawanda zai ganeki. inata wutsil wutsil ina dan kuka. Muka shiga,. Mutum daya ne a Reception na rufe ido da bayan shi wai kar yaga fuskata. Ina ta dukan bayan Shamaki, wani yana tsaye bakin wata kofa shine ya bude mana kofa sannan suka sake yin magana ya shiga ya rufe kofar ya zube ni kan gado. Na diro da sauri nace nifa bazan tsaya ba, ni ba karuwa bace. Kalmar ta fusata shi da alama. Yace karki fusata ni Baby. Nace nafison ka fusata din ko ka kai ni gida. Hajiya ma nasan yanzu tana jiranka kuma zan shafa mata maganinta a kafa.
Ya turani na fada gadon ta baya, na san a raina ni dai bazan yarda ya kwanta da ni a Hotel ba, domin hakan zunubi ne.
Ya cire kayansa ina ta kuka, ya fizgo ni, rigata ma da ta bashi matsala yagata yayi. Karfi ya nuna min ko ince Shamaki fyade ya yi min kuma har saida ya min rauni. Na kasa tashi, shi kuma juya min baya ya yi ya kama bacci. Nima dai bansan lokacin da baccin ya yi gaba dani ba. Farkawa na yi na ganshi yana salla. Na tashi zaune da sauri, sai lokacin na ke karewa dakin kallo, ya yi matukar kyau, kamata ya yi ace wannan dakin a gidan sure yake. Na tashi na sauka ina dingishin iskanci waini amin fyade, duk da ina jin zafi amma bai kai yadda na dauki abin ba. Na dube shi Nace ko isha'i bai yi ba ashe amma ya iya kawo ni Hotel Allah dai ya sani kuma bazai rubuta min zunubi ba.
Na zauna baki gado ina mitar gashi duk an jima mutum ciwo. Bini da kallo yana murmushin mugunta.
Sannan yace in kin gama mitar sai ki tashi kiyi sallar asbahi tunda kin ja mana makara gashi nan yanzu har shida ta yi. Na mike da sauri na dafa kirji nace wai kana nufin gari ya waye!? Yace "Ina wayar ki tana mota da kin duba lokaci yawwa kali agogo gashi nan. Na kalli bangon da ya nuna da sauri, take na rikice nace na soma kukan gaske da hawaye masu dumi, nace Shamaki ka kashe ni, yanzu me zan fadawa Hajiya fisabililllahi! Yace ke ki ka ja komai da kin tsaya awa daya kacal ko biyu zamu tafi, kina ta wani ihu wai ke ba karuwa bace, shikenan dan karuwanci aka gida Hotel ke ma kina cikin sahun mutane marasa fahimta, to ko a Saudiya ki ka je ina zaki sauka in ba Hotel ba?"
Na kalle shi a makka ba gidaje bane na dama kowa ya zo zai kama bide ya shiga?
Ya yi dan murmushi waye ya fada miki wannan din to a Hotel ake sauka, zaki je ki gani wa idon ki.
Sannan kuma ni mijin ki ne dan munzo nan mu dan huta sai kawai mu samu zunubi, irin ladan da muka samu a dakina ko naki irinshi ne dai zamu samu a nan.
Amma ke jiya na san baki samu komai ba kila ma sai zunubi amma na yafe miki. Jikina ya yi sanyi nace to ai kaine baka gaya min ba. Ya harare ni, in fada miki me bayan kina ta hauka, kuma zaki ce duk baki san komai ba kinyi makaranta fa. Na turo baki, nace dan nayi makaranta ta gwamnati ce ina cikin lokon mu ni ba kallon TV ba ba jin radio ba, garama ina dan karance karance. NI ban san me ake ciki ba. Yace to yanzu jeki kiyi salla dai." Na shige bandaki, na kalli ko ina gwanin shi shi'awa, na kalli kaina a madubi nace ni Baby a Hotel yau. Nayi wanka na yi alwalla na fito. Na saka siket na daga rigata nace to ni yanzu sai ka biyani rigata. Ya daga rigar tayi kaca kaca, ya yi murmushin mugunta yace, ni ma dai jiya na yi wa wata yarinya fyade, kuma fa naji dadin hakan. Kinsan namiji yana son style kala kala. " nace Ni baruwa na yanzu kasan yadda zakayi da ni. Ya cire janfar da ke jikinsa sai singiletin shi yace "Sa wannan ni sai inje da malun-malun tana mota."
Na dauka na saka a jikina. Ya kalle ni ya yi murmushi ya kuma Hajiya ba a yi mata karya. Na tashi na ja baya da sauri gaskiya kai zaka fada mata. Cikin shagabar da bansan na hi ba na yi maganar.
Yace "In ba haka ba fa? " Na soma kuka nace sai dai ka kaini gida. Ya tashi ya fara daura agogonshi yana fadin can gidan sai kice musu munje Hotel kin ki bani hakkina na yi miki fyade mun kwana gashi Hajiya bata sani ba." Shikenan said Umma ta raka ki gida. Ya karasa maganar cikin dariyar da yake ta kunshewa. Nace kenan dariya ma ka ke yi ko? Yace "Kowa tashi ta fisshe shi." Ya fada yana hada kan wayoyin shi. Na zauna bakin gadon nace In kuwa haka ne gara in zauna a nan. Yace "Shabiyu tana cika zasu kore ki ne, su gyara dakin su. Ya zura takalmi ya dauki yagaggiyar rigata ya ce shike nan ni na tafi....
🖊️🖊️🖊️
Da gudu na tashi na bi bayansa har ya shiga mota ya tada, ban damu da rigarsa da ke jiki na ba. Koda dai mutum biyu ne a Reception din, na nufi motar yana kallo na sai ya yi hanyar waje.
Na kwasa da gudu na nufi gunsa, na bude gaban motar na shiga, da alamu dariyarsa ya sha domin har lokacin ita yake kunshewa. Nace da gaske da tafiya zaka yi?
Yace "To me zai hanani tafiya tunda kince ke bazaki tafiba. "
Nace tsoro nake ji Hajiya zata yi fada, da wane ido zan kalli Hajiya, sannan kuma dubi yadda ka maidani kayan ka ne a jikina fa..
Ya ce "Ki dai shirya bayaninki tun a nan kafin aje ki kasa magana. Ki fara shirya fada mata inda ki ka kwana da kuma dalilinki ". Nace mu fara biyawa ka saya min ko doguwar riga ce in baka taka ka saka mu fara zuwa gida a mutuce. Ya ce ba inda zani.
"Ki barni inji da me zan fadawa Hajiya kema ki tanadi abinda zaki kare kanki." Nace kai ne zaka fada mata tunda kai ka ja komai, ni ban taba zuwa Hotel ba. Ya sake fafin kowa tashi ta fisshe shi. " Na kifa kaina a cinya takaici ya ishe ni. Ga tsoro ga kunyar Hajiya da zanji, ko yaya zata kalli abin? Nasan bazata ji haushin danta ba, abin akai na zai kare.
Muna shiga kan ya gama fakin na kama kiciniyar bude kofa. Yace ki tsaya in fada miki wata magana, na kalle shi ya daure fuska, in har ki ka yarda na rigaki zuwa gaban Hajiya ke ce zakiyi yi mata bayani." Nace Allah ni ba zaka dora min laifi ba. Na soma kawo ruwan hawaye. Yace Au kuka zaki yi to shikenan ki yi. Daga nan zata fara gane cewa baki da gaskiya. "
Ya bude mota ya fita. Nima na fita na bi bayan shi da sauri a falon daf dana Hajiya muka hadu. Ya kalle ni, "Gabana faduwa yake. " Ya fada yana kallona. Na tsoro ya kara kamani, in shi yana jin tsoro ni kuma yaya kenan? Ya sake fadin "In har na riga ki shiga ke ce wadda zaki yi wa Hajiya bayani.
Da sauri na tura kofa na shige kafin ya rufe baki.
Kamar yadda na zata Hajiya tana zaune a inda take salla da carbi a hannunta na shiga da sauri, na zauna a gefen ta. Ta waiwayo da sauri kamar ta firgita da ganina, ta kuma kafe ni da ido. Nace sannu Hajiya. Ta dauke fuskarta ba tare da ta amsa min ba.
Jikina ya yi sanyi ko ba a fada min ba nasani dole ne in dauki Wannan Zunubin lokacin Ya yi sallama kamar wani salihi, ga mamakina sai Hajiya ta amsa sallamar harma ta kara da fadin an shigo. Ya iso ya zauna daf da ita ya yi kasa da kai yana gaishe ta. Ta amsa cikin fara 'a. Ya kalle ni ya yi wani murmushin mugunta, sannan ya dora min yagaggiyar rigata akan jikina ga rigar ki je ki cire min tawa. Na yi zaton Hajiya zata tambaya dan in samu in wanke kaina amma sai naga ta kalli rigar sannan ta sake kallon ta jikina. Sai kuma tace masa, in ka shiga ina bukatar takardun filin nan da aka siya a Fandanka? Yace suna jakata a kawo su ne? Tace ka fito da su domin a kwai wata magana akan gurin jiya lauya ya kira ni nace ya same ni a gida in kuma zaka fita kasuwa yau sai ku karasa can. Shamaki Yace zamu fita kasuwa sai dai kuma yau ina da meeting kashi uku ki hadu da lauya kawai. Akwai wadannan 'yan China da suke son stor dinmu na Sharada a nawa ganin gara mu saida musu tunda kinga bama komai a gurin, kuma zai yi daraja saboda su suke bukata. Ni dai na mike na nufi dakina a sabule.
Na shiga ban daki na dan gasa jikina da ruwan dumi sannan na canza kayan jikina na hau gado na kwanta, ina tunanin wannan zama namu. Ina ta fadi tashin ganin cewa na samu zama na har abada amma wani lokacin sai inji jikina ya yi sanyi. Kamar dai yanzu da muka yi laifi amma sai ta wanke danta fes.
Na fita lokacin karin kummalon su ya yi, Na samu Juma tana jere abinci, na shiga cikin dari dari, Hajiya tana zaune a kan kujerarta Shamaki a gefe ga takadu kusa da shi yana sanye da Jallabiyya. Na yi wa Hajiya sannu. Ta amsa ba tare da ta kalleni ba. Na fara da goge teburin ta na jikin kujerar ta wanda da shi take cin abinci. Nace me za a saka? Tace kunu zata sha na gyada. Na san abubuwan da zan hada mata in kunu zata sha. Na hada mata komai. Tace wa Shamaki "Ya kamata gobe a tashi da azumi a gidan nan tunda bikini salla ya kare sai a yi sitta shawwal ko? "
Shamaki ya ce wannan tsuntsuwar data sani a gaba tin washe garin salla na fara, in nayi yau da gobe na gama". Na kale shi ya zuba min ido. Na yi kasa da murya nace na ci maka bashi ne da zaka zura min ido?
Wai da Hajiya ta ji mu sai ya daga murya. Me ki ka ce? Na kalli Hajiya ta maido hankalinta garemu kuwa. Nace me zakaci in zuba maka? Yace ina azumi fa kin sani. "
Nace Baka yi sahur yau ba, gaskiya bazaka yi dore ba, ka bari sai gobe tunda ka ga ai ba wai farilla bane. Yace "Baki tashe ni ba ne ai." Na harare shi, haka ma zaka ce? Ya yi murmushin mugunta, yace ashe fa gurin maulidi muka kwana. Hajiya ta kalle ni, ni kuma na kalle shi ya kauda kai. Azuciya ta nace karyar da ya yi kenan to wane maulidi kuma a salla.
Ya katse ni, "Dama ke ki ka takura inyi in gama amma yanzu zaki zo da zamiya. Na soma zubo masa kunu, sai na tuna da wayon da nake yi wa Jafar din mu in ya ki cin abinci a ramadan ya ce wai shi yana azumi. Sai in zuba masa kunu in ce ya sha baya karya azumi..
Na mika wa Shamaki kunu cikin tsokana na ce kasha wannan baya karya azumi. Ya karba ya kurba, nace Allah ya yafe maka. Ya ce "Ameen amma alhaki a kanki.
Ke ki ka sa na karya azumi. Ya dauki kosai daya da na zuba na tura masa. Ya gutsira yace na sani fa bakya son insha wahala ne ko? "Nace ta yaya zan so ka sha wahala, amma kai kana son insha ai tunda kai da kanka ne ka shayar... Ya nuna min Hajiya da ido, ya gane maganar jiya zanyi. Na rasa wani lokacin in muna tare da Shamaki gaba daya sai in manta da akwai wani a gurin.
Juma ta sake shigowa tana fadawa Hajiya cewa man shanu ya kare tace za a kawo shi yau kuwa domin miyar danyar kubewa nake son ci. Tace to sai an kawo naman rago shima ya kare.
Hajiya tace a yi ta kaza.
Na tuna da irin yadda Tsohuwa ta bani labarin yadda Hajiya Zeena ta ke yi wa Hajiya Gwamma abinci da kanta, sai naji ina shi'awar in aikata hakan. Na ce Hajiya ina son in roki wata alfarma don Allah. Ba Hajiya ba hatta Shamaki ya dakata dan ya ji me zance. Ita kuma Hajiya da alamu yadda na yi maganar cike da kwarin gwiwa shine ya sa ta dakata, ko da dai na lura Hajiya tana son jin magana ko tsegumi amma bata nuna cewa ta damu da hakan.
Ta ce ina jinki. Nace ina son ki yi min izini inna dafa miki duk abinda ki ke so. Ta dan yi kasake, sannan tace "
"Ai baki iya girki ba, amma zan baki dama ki fara koyon girki a gurin su Juma, in hannunki ya fada zuwa lokacin da ki ka cika shekara daya sai mu duba muga ko zaki iya din ko? Haka ya yi miki? "
Nace Na gode Hajiya, insha Allahu zan sa hankalina in koya. A zuciya ta nace in banci Jarabawa ba shikenan. Kukan Anisa ya dauki hankalinmu ta karaso da gudu Shamaki ya bude hannu amma sai ta fada Jikina tana fadin Mommy kinga Meema ko ta shanye min icecream kuma ba ni ce na bata ba."
Shamaki zai yi magana Hajiya ta daga mishi hannu alamun ya yi shiru ta gefen ido na lura da su.
Na rungume ta, nace, yi hakuri, na fara share mata hawaye. Nace. ba na fada miki Yaya meema zaki ce ba? Tace Yaya Meema ta shamin abuna. Nace zomuje daki zan baki wani amma ki ce kin yafe mata wancan din. Tace "e na yafe amma mommy za ki yi mata fada? " Na ce a a zan yi mata nasiha ne zakigani bazata kara ba.
Na mike
0 comments:
Post a Comment