A mota ɗaya suka tafi ran kowa babu daɗi, dan haka motar ta ɗauki shiru sai driver daketa aikin tuƙi har suka isa Shira Hospital.
Tuni AK ya tanadi likitocin da zasu aikin harsu uku domin samun gamsuwa akan abinda zai fito, dan haka suna isowa suma su Mmn Sadiq suka iso ɗauke da Little.
Yanako ganin AK ya maƙale masa, duk da ɓacin ran da AK ke ciki sai da yay murmushi yana mai rungume little a jikinsa. Ganin yaronma da yayi sai yakeji a ransa ALLAH ma yasa ya kasance nashi ɗin, dan har cikin ransa wata irin ƙauna yake masa mai ƙarfi da saka zuciya nutsuwa.
Cikin mutunta juna suka gaisa, inda mamaki ya cika Dr Mahmud saboda ganin Abba. Shima Abba daya ganesa sai wani tunani yazo masa. Cikin kasa jure abinda ke ransa yake tambayarsa ko ina bawan ALLAHn nan daya sakama little sunansa?.
Kai tsaye Dr Mahmud dake dariya ya nuna AK, “Baba ai gashima zaune, ina takwaran nasa kuwa? Nasan ya girma yanzun ko?”.
Da sauri Abba ya kalli AK da Little ke a jikinsa zuciyarsa na bugawa. Cikin ɗan rawar murya yace ai ga yaron nan a hannunsa”.
Ba Dr Mahmud ba, hatta AK sai da zuciyarsa ta harba. Yay saurin duban Abba da faɗin, “Uncle kana nufin kaine wanda ya bani damar zaɓama yaro suna shekara uku data shuɗe?”.
“Tabbas nine kuwa. Kuma wannan shine yaron”.
Sosai maganar Abba ta sakasu jin shock su duka. Baffah dake saurarensu ya nemi jin ƙarin bayani. Dr Mahmud ne yay masa bayanin komai har yanzu firgici da al'ajabin kamannin little da AK na bayyane a fuskarsa.
Murmushi baffa yayi yana jinjina kansa. Sai dai komai baiceba yabarma zuciyarsa. Dan yama gama yarda AK na ɓoye masa wani abune game da yaron kenan, inba hakaba yaya akai hakan ta faru? Tunda a wannan zuwan basusan yazoba sai a shanun ƴan talla yaji. To lallai kam zaiyima tufƙar hanci, dan yama gama yanke hukunci saura zartarwa.
Baffah ne ya dakatar da wannan hasashen su Dr Mahmud suka shiga aikinsu. Duk wani gwaje-gwajen daya dace akan ƙwayoyin haluttar little da AK akai musu. Abinka da masu abu, ba'a wani zauna wasaba suka shiga ganin sun tantance komai dan Baffah yace bazasubar asibitinba sai da result.......
_________________________★
*DANYA*
A lokacin da gwajin ƙwayoyin halitta ke gudana acan Shira Hospital tsakanin AK da Little anan danya kuma baƙuncin Baba su Inna suka samu da farar safiya babu zato babu tsammani.
Duk suna zaune a tsakar gida ƴan barka na shigowa jefi-jefi da ƴan gulma. Karima na ɗaki kwance ita da ƴar jinjirarta tana kwasar kuka akan abinda ya barota da Kaduna, dan wahalar ciki tasa bata samu damar nazari akan komaiba sai yau da take jinta sakayau.
Tinene na kwance a ƙofar ɗakinsu wai ƙirjinta da kanta na ciwo, tun safe data tashi da abinda ta wayi gari kenan. Sai Sa'a daketa kaikawon yin aiki ita da Yaya Gajeje. Inna kuma na zaune kusa da Tinene tana gyaran gyaɗa da Yaya Gajeje tazo da ita gidan domin yin miya.
Sallamar mace da sukaji ya sakasu ɗan juyowa kusan su dukansu dan duk zatonsu ƴan barka ne ko cikin dangin Babawo dakan zo jefi-jefi, dan innarsa ma da tace zata dawo tun jiya har yau basuga ƙeyartaba. Sai dai ta aiko musu da kayan kunun da tace dana barka kuma kamar yanda uwar miji keyi a al'adar ƙauyen.
Ƙyaƙyƙyawar mace mai tarin kamala da ƙwarjini ta sake maimaita sallamar datai musu ganin duk sun zubo mata idanu basu amsaba. Yaya Gajeje ce tai ƙarfin halin amsawa da cewa, “Maraba, bismillah shigo baiwar ALLAH duk da dai bamu wayekiba”.
Murmushi matar tayi tana ɗan juyawa bayanta jin motsin takowar abokin tafiyar tata. Kafin ta samu damar bama Yaya Gajeje amsa Baba ya shigo shima da sallama a bakinsa. Duk da ƙyawun da yayi cikin ɗanyar shadda fara tas da ƙiba daya ƙara da haske hakan bai hana iyalan nasa shaida shi ba.
A take fara'ar fuskar Inna ta ɓace ɓat sai gabantane ke wani irin bugawa da sauri-sauri kamar zai buɗe. Cikin rawar murya tace, “Malam?!”.
“Na'am Asabe”. Ya amsa kansa tsaye yana kallon cikin ƙwayar idanunta.
Baya tai a tsorace zata zube dan ruɗani, a dai-dai sansa du Yaya Gajeje ke haɗa baki ita da Sa'a da Tinene data tashi zaune da ƙyar wajen kiran “Baba!”.
Nanma kai tsaye ya amsa musu da “Na'am ƴaƴana”.
Ai tuni Sa'a ta kwasa da wani irin gudu tayo kansa batare data saniba. Ta faɗa jikinsa tana fashewa da wani irin kuka maiban tausayi. Hannu biyu yasa wajen riƙe abarsa yana murmushi, ya miƙama Tinene hannu itama. Da sauri tayo kansa duk da halin ciwo da take a ciki itama ta shige jikinsa.
Hayaniyarsu tasa Karima fitowa itama. Ganin Babansu yasata kware baki cike da firgici ta kwala ihun daya jawo hankalin maƙwafta suka fara leƙe ta kantaga. Sai gashi cikin ƙanƙanin lokaci gida ya ɗauki harama. dan tuni ashe jama'ar gari sunga baba sanda yake shigowa garin tare da matarsa.
A take gida ya ɗauki murna, dan tuni dangin baba su Gwaggo Laritu harsun iso jin labarin dawowar ɗan uwansu. Sai koke-koke akeyi na farin ciki. Da ƙyar aka samu gidan yaɗan natsa aka kawoma Baba da baƙuwarsa ruwa. Babu musu suka amsa suka sha dan sunada buƙatarsa.
Baba Rabilu cikin kasa haƙuri yace, “Yaya gaka da baƙuwa kuma bamusan wacece ba?”.
Murmushi baba yayi yana mai kallon ƙyaƙyƙyawar matar, zuciyarsa fes da farincikin daya bayyana a saman fuskarsa yace, “Itama yayarku ce. Dan tazama ɗaya daga cikin zuri'armu tunda ta kasance Matata harma da tsohon ciki gashi nan”.
Cikin mamaki da nuna bayyanannen farin cikinsu suka shiga sake mata gaisuwar girmamawa. itako cike da fara'a da mutuntawa a garesu take amsawa. Babu wanda ya lura a cikinsu sai jin faɗuwar Inna sukai timmm a ƙasa. Dan hatta da Tinene sai da ta gaida matar da baba ya kira da matarsa. Karima ce kawai ta wani gwalalo idanu tana kallonta.
Kusan su duka kan Inna sukayi, banda Baba da ko motsi baiyiba sai dai ya kalli wajen. Ruwa Sa'a ta ɗebo da sauri ta kawo, Gwaggo Laritu dake riƙe da Inna ta amsa ta shafa mata a fuska. A take ta kawo numfashi tana binsu da kallo. idonta ta sauke akan baba da Amaryarsa. Babu zato sukaji ta fashe da kuka kawai ta fara sambatu
“Dan girman ALLAH na roƙeku ku taimakeni ku hwaɗa mani gaskiya, kuce dani mahwalki nake ba gaske baneba, na shiga uku ni Asabe. Yanzu malam irin sakayyar da zakaimin kenan akan wahalar ganin ka dawo gida da nakeyi tsahon shekaru? Yanzu malam duk hwaɗi tashin da nake akanka karasa da abinda zaka dawo gareni sai kishiya? Na shiga uku na lalace ni Asabe. Shikenan watan lalacewata ya tsaya kuma sai abinda ALLAH yayi. Ku dubetahwa jama'a kamar aljana. Wlhy tahi Hauwa kyau da ƙuruciya.....”
Ta ƙare maganar da ƙara jan wani nannauyan numfashi alamar ta sake suma.........
____________________________★
*_KANO_*
Bayan dogon zaman jira dasu AK sukasha sakamakon gwajin DNA ya fito daga likitocin guda uku, Batare da ko su Dr Mahmud sun dubaba aka mikama Baffah. Shima ɗin bai buɗeba ya sake miƙama Dr Mahmud dan yasan amintaccen AK ne. Kuma shina ya yarda dashi ɗari bisa ɗari.
Dr Mahmud da duk al'amarin yake neman rikita masa kai ya amsa ya buɗe takardun ɗaya bayan ɗaya zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri-sauri. Sai da yayma takardun kallon kusan sakan biyar kafin ya ɗago ya ɗan dubi sashen da AK ke zaune rungume da Little dake barci yanzun. Cikin wani irin rawar murya da firgicin abinda ya gani ya maida kallonsa ga takardun yana magana da rawar harshe.
“Ba lallai ku fahinci duka bayanan cikin takardun ba saboda wani abun daga bincike likitocine kawai. sai dai ina mai sanar muku cewar zan faɗi gaskiyar abinda na gani kamar yanda baffa ya bukata tsakanina da ALLAH”. Ya ɗan sharce gumin daya taru masa a goshi da cigaba da faɗin, “B...Baffah sakamakon duka takardun ya nuna ya..ron... Na na na AK ne, dan duk ƙwayoyin halitarsa babu banbanci da yaron kamar yanda ya biyosa a kammani”. Ya ƙare zancen da tsananin raunin harshe dana zuciya.
Kusan a tare suma su Baffah zukatansu suka buga. AK dakejin kansa na neman tarwatsewa ya ƙanƙame little a jikinsa yana rumtse idanunsa da matuƙar ƙarfi, har takai yaron ya farka daga barci yana ƙoƙarin fara kuka saboda jin matsar da akai masa.
Yanda yayi ɗinne yay matuƙar tada hankalin Dr Mahmud da gaba ɗaya hankalinsa ke akansa. Da sauri ya miƙe zuwa garesa yana ambaton sunnsa. Hakanne ya fargar dasu Baffa ruɗani da ɗimuwar da suka shiga suma duk sukai kansa.
Da ƙyar suka iya ɓanɓare little daga jikinsa, Baffah da Abba suka riƙe AK ganin jikinsa na wani irin rawa maiban mamaki da tsoro, cikin ƙanƙanin lokaci kuma duk sai gaɓoɓinsa suka saki alamar ya suma.
Wannan shine tashin hankali wanda ba'a saka masa rana, dan kuwa dai Baffah ji yay tamkar ya fasa ihu dan tashin hankali goma da ashirin, yana matuƙar ƙaunar AK a ransa. Dan yana ɗaya daga cikin ɗa mafi soyuwa a garesa, sai dai yana dannewa ne gudun rarraba kan ƴaƴansa.
Da ƙyar suka iya ɗagasa zuwa gadon duba mara lafiya dake a office ɗin Dr Mahmud. Mmn Sadiq kam kuka take sosai dan gaba ɗaya ta gagara fahimtar wannan al'amari maiban ruɗani da al'ajabi........
*_BAYAN WASU AWOYI_*
Bayan wasu taƙaitattun awoyi aka samu nasarar farkawar AK da tun ɗazun ya farfaɗo daga sumar da yayi. A hankali ya buɗe rinannun idanunsa ya saukesu akan Baffah dake zaune riƙe da hannunsa. Sai Abba dake ta wajen ƙafafunsa shima a zaune. Mmn sadiq kam ta wuce gida tuni tare da little dan taje ta huta itama gudun kar taje ƙasa. Dan kallo ɗaya zakai mata ga gano tsananin tashin hankali da ruɗaninta.
Kallonsu yayi ya maida idanun ya lumshe a hankali yana wani irin murmushi da baida maraba da kukan ƙunar zuciya. Idanunsa a lumshe yace, “Baffah nasan ba lallai ku yarda daniba akan bansan yaya akai na samar da Abdul-Mutallab ba. Domin ni kaina na kasa yarda da kaina balle ku da zan faɗamawa. Sai dai ku sani lallai ina cikin *_MAKAUNIYAR ƘADDARA_* babu wani haske da zai haska min idanun ganinta kuma sai UBANGIJINA da haƙurin fahimtata da zakuyi na ɗan wanu lokaci dazanyi ƙoƙarin ganin bakin zaren, b.........”
Saurin katsesa Abba yay ta hanyar faɗin, “Ya isa Adnan. A yanzu halin da kake ciki baya buƙatar duk waɗanan maganganun. Dan Mahmud ya tabbatar mana da jininka yayi ƙololuwar hawa sama. idan kuma ka matsa da yawa za'a iya samun matsala. Mu dukanmu nan musulmai ne, muna kuma iya fahimtar yaran ƙaddara ko jarabawa, suk da dai ita wannan tazo mana a makance. Dan kai da Zinneerah ne ya kamata muji amsar tambayoyinmu a gareku, sai kuma gashi kuma neman amsoshin kukeyi a karan kanku. A ganina mafita ɗaya ce da shawara ta rage mana Alhaji”. Ya faɗa yana duban Baffah.
Kai tsaye Baffah yace, “Karka damu Alhaji Abubakar, kai maganarka kai tsaye dan kaima ubane mai cikakken iko akan su Adnan da wannan matsalar tasu da ni ta sakani a babban ɗakin duhu bama na makanta kawai ba”.
Murmushi Abba yayi, cikin son tausasa fushin Baffah da yake hangowa yace, “Nagode Alhaji Kabeer, abinda nakeson faɗa kai tsaye shine, mu koma ainahin ƙauyen Danya ko zamu samo bakin zaran inda matsalar take, dan a binciken da nayi wancan karan bazai gamsar damu ba saboda rashin samun mahaifin Zinneerah da nayi, sannan ƴan uwansa duk sunƙi bani haɗin kai akan wani dalilinsu da ban saniba. To amma sai nake dangantashi da fushi, sai dai ina fata da tsamanin insha ALLAHU zuwa yanzun sun huce. Maybe mu samu wani bakin zare da zaisa shima Adnan ya fahimci daga inda matsalar take ko zai tunano wani abu tunda dai babu wata hanyar samuwar ɗa sai da nasaba mai ƙarfi. Amma yaya kuka gani, dan yanzu ni wannan hasashena ne kawai”.
“Maganarka nakan hanya Alhaji Abubakar, kumani wlhy na gamsu da ita ɗari bisa ɗari”. Baffah ya faɗa yana miƙewa tsaye.
Zaune AK ya tashi da ƙyar, cikin son danne damuwarsa yace, “Uncle wannan shawaran naka yayi dai-dai, nima na gamsu da ita. Sai dai dan ALLAH ku gafarceni idan na ɓata ranku”.
Da sauri Abba ya girgiza kansa. “Ka kwantar da hankalinka Adnan kaji, ALLAH zai warware mana komai cikin sauƙi”.
Kai kawai AK ya ɗaga masa, dan yasan Baffah a ƙullace yake da shi. Duk yanda Dr Mahmud yaso riƙesa a asibitin yaƙi yarda, dole ya barsa suka tafi gida shi da Baffah Abba ma ya nufi nasa gidan. Bin bayansu Dr Mahmud yayi da drip da magunguna dan yasan AK na buƙatar hutawa na wasu awoyi ko hankalinsa zai dawo jikinsa.
Tunda suka taho ko sau ɗaya Baffah bai yarda sunyi maganaba. Shima bai iya cewa dashi komaiba saboda ciwon kai dake damunsa har yanzun.
Da suka shigo gidanma baffah cayay AK yaje shi yana buƙatar hutu. Ganin Dr Mahmud biye dasu yasa baiyi musu ba ya nufi sashen Hajiya iya shima. Acan Dr Mahmud ya samesa. duk yanda yaso ƙin yarda ya saka masa drip ɗin haka Dr Mahmud ya dage sai da ya saka masa tare da allurar barci mai ƙarfi. Aiko cikin amincin ALLAH sai gashi a ƙanƙanin lokaci barcin yay awan gaba dashi.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
________________________
*Page 40*
...........Da farko Baffah yaso kira ya sanarma Hajiya iya komai, sai dai a bisa wani tunaninsa kuma sai yace bara ya bari har zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu da yake da burin yanke hukuncin daya dace ya kuma san Hajiya iya zataji daɗi sosai. Bai sanarma kowa mike faruwaba a cikin matan nasa, ya dai nema ƙanwarsa Bilkisu a waya sunyi magana, anan nema take sanar masa itama gobe idan ALLAH ya kaimu takeson sake zuwa london ɗin domin duba jikin hajiya iya, tanata neman wayar AK ma bata samuba ashe ya shigo 9ja ne. Tace amma tunda wannan ta taso bara ta dakata harsu dawo daga danya, dan dama tanason su tattauna akan ɓoyema Ahmad rashin lafiyar Hajiya iyan da sukayi.
Cike da so da ƙaunar ƴar uwarsa Baffah yace, “Babu damuwa Bilkisu, kiyi haƙuri na kashe wannan ƙurar duk da nasan tawuce kasuwar gobe, dan yanda Adnan ya dage cewar bai aikata wani abu akan samuwar yaron nanba hankalina na tashi, inaji a raina kuma kamar akwai wani abu ɓoyayye da bamu saniba”.
“Gaskiya kam Yaya al'amarin yana buƙatar bincike, baka shaidar ɗan yau amma koni dai inaji a raina Adnan bazai aikataba, to amma jin cewar gwajin DNA ya tabbatar da ɗan nasane yasaka jikina duk yayi sanyi gaskiya. Amma inaga zan shigo zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nan ɗin kawai”.
“To ALLAH ya kaimu da rai, kizo ɗin kozanji sanyi a raina na samu abokin shawara nima”.
Daga haka sukai sallama. Idan barci ya figi baffa a wannan dare sai dai ɓarawo. Hakama mmn Sadiq acan barci ya gagareta. Danma Abba nata mata nasiha da lallashi harya samu taɗan saki jikinta saboda kar matan gidan su fahimci akwai matsala.
*WASHE GARI*.
Washe gari Alhmdllh AK ya tashi garau a zahiri. a cikin zuciyarsa kuwa shi kaɗai yasan mi yakeji gameda son tunano ko ya taɓa aikata wani abu makamancin wanda yake tuhumar kansa akan samuwar little. Sam bai iya tuna komaiba balle ya gano, dan haka ya ajiye komai a ransa yay shiri kamar yanda baffa yace.
Yayi ƙyau matuƙa cikin ɗanyar shadda fara tas da taji ɗinki mai ƙyatarwa da ɗaukar hankalin mai kallo, ya murza hula a kansa wadda ta sake ƙawata tsarin adon nasa da bayyanarsa cikakken bahaushe. Turare ya saka ya fito yana baza ƙamshinsa mai sanyi da daɗin shaƙa. Yayi mamakin cin karo da matasan ƙannensa suma cikin shiri, sai dai baice komaiba ya shiga amsa gaisuwar da suke masa cikin girmamawa.
Baffa ne ƙarshen fitowa sanye shima cikin tashi ɗanyar shaddar, fuskarsa a sake tamkar babu damuwar komai tattare da shi, har hakanma ya bama AK mamaki da tsoro, dan tun yana yaronsa ya gama karantar irin wannan yanayin na Baffa. Idan kai masa laifi ya nuna kamar bai damuba to lallai akwai abinda yake shirya maka kuwa.
Motoci suka shiga, Baffa shi kaɗai sai drivern sa, dan acewarsa zasu ɗauki Alhaji Mansur babban amininsa a gidansa. Sai yazam su Moos'ab sun taru a mota ɗaya su huɗu. AK na shirin shiga wata motar shi kaɗai sai ga Dr Mahmud ya iso. Hakan yasa ya shiga motar Dr Mahmud ɗin kawai da shima dai da alamar shirin tafiyar yazo gidan dama.
Duk da AK cike yake da mamakin wannan gayya sai baice komaiba. Sun dai gaisa da Dr Mahmud ya tambayi yaya ƙarfin jikinsa daga haka sukai shiru, Dr Mahmud nata juya abinda yakeso su tattauna a ransa ya kasa furtawa, dan duk da AK abokinsane yana girmamashi akan wasu dalilai masu yawan gaske.
Sai da suna gab da fita cikin garin kano zasu kama hanyar katsina AK ya sake fahimtar bayan motocinsu uku akwai wasuma biye dasu kusan guda uku. Cikin kasa jurewa yace, “Wai nikam wannan gayyar ta minene Baffah yayi?”.
Ɗan dubansa Dr Mahmud yayi, cikin rashin fahimtar inda zancen nasa ya nufa yace, “Gayya kuma ranka ya daɗe?”.
“Uhm, ko bakaga motocin dake biye damuba?”.
Ta mirror Dr Mahmud ya duba bayansu, a nazarce yace, “To inaga dai ba tafiyarmu ɗayaba gaskiya”.
Shiru AK yayi duk da bai gamsu da hakanba, sai ma ya jawo wayarsa kawai ya shiga daddanawa.
Tafiyar da bata gaza awa ɗaya ba suka iso gidan mutum ɗaya, kai tsaye hanyar kusada suka shiga, a lokacin kuma AK ya sake tabbatar da tafiyarsu ɗaya da motocin nan, amma sai yay shiru bai sake magana ba. Abinka da lafiyayyun motoci ga kuma lafiyayyar hanya cikin ƙanƙanin lokaci suka iso cikin kusada. Basu wani tsayaba suka ɗauki hanyar Danya.
Haka kawai AK ya samu kansa da nutsuwa a kallon hanyar zuciyarsa na masa wasu tunani daban akan rayuwar Zinneerah a ƙauyen, rashin ƙyawun hanya ya ɗan jasu lokaci mai tsaho kafin su shigo cikin ainahin ƙauyen Danya. Duk da ba safiya bace garin akwai mutane sosai, dan lokacine na shigowar farkon damuna mazan garin nata dawowa gida domin haramar noma.
Sosai idanu suka dawo caa akan dalla-dallan motocin kowa na tunanin daga ina haka?. Wasu suce ƴan siyasa wasu suce daga fadar sarkin katsina ne. to basu dai da tabbas, duk da kuwa kai tsaye Abba gidan maigari ya nufa dasu, dan shine jagoran tafiyar tasu. A ganinsa kuma hakan shine yafi cancanta da wannan tawagar tasu dan bayaso ai musu irin wulaƙancin da akai masa a wancan zuwan.
Su maigari suna zaune a bishiyar ƙofar gidansa shi da fadawansa sukaga motoci galla-galla na tsayuwa. Ba karamin kaɗawa hantar cikin maigari da ƴan fadarsa tayiba. Dan duk zatonsa samame aka kawo masa daga fadar sarikin katsina. Duk da yasan baya aikata wani mummunan al'amari ga ƴan garinsa sai da yaji tashin hankali. Bai ƙara rikicewaba sai da su AK suka fara firfitowa.
Daka gansu kaga manyan ƙasa masu ci da tsinin allura, dan duk sun jiƙu cikin shaddoji masu maiƙo da ɗaukar idanun mai kallo. Abba ne ya matsa inda suke yaɗanja maigari dake a ruɗe gefe sukai ƴar magana. a take bakin maigari ya washe ya shiga sakin tagwayen ajiyar zuciya. Bai tsaya jan jikiba yasa ƴan fadar tasa shiga cikin gida suka fara fitowa da tabarmi sabbi ƙal tare da manyan dardumai aka shishshimfiɗa a babban zauren maigari dake share ƙal ga sanyi mai saka nutsuwa gaduk wanda zai zauna.
Duk ciki suka shiga, akabar Baffah da Abba da Alhaji Mansur da Alhaji Yusif a waje suna son yin magana da maigari, dan Alhaji Yusif Mande da Alhaji Mansur Tofa manyan aminan Baffah ne da kowa yasani, tun kuma a daren jiya ya sanar musu abinda zasuzo yi anan ɗin.
Abba ne yayma maigari bayanin nason ganin dangin Malam Sule baduku. Da kuma abinda ke tafe dasu. Jin sunan Zinneerah ya saka maigari jin dunbin daɗi a ransa, dan shi wlhy yama manta da yarinyarnan sam a rayuwarsa. sai dai yau dalilin ambatonta yasakashi farin ciki musamman da yaji dalilin zuwa waɗanan manyan mutane. Bakinsa a washe yace, “Ai Alhmdllh ma kun yanka akan gaɓa Alhaji, dan Malam Sule ɗinma ya dawo garin jiya-jiya, zanma iya cemuku yanzu da safen nan sukabar gabana shi da fitinanniyar matarsa akan rikici data tada dan yazo da sabuwar amarya daga Niger. Inaga yanzu bara na aika a kirashi shi dasu Rabilun ku zauna ku huta”.
Sosai su Baffah sukaji daɗin jin cewar mahaifin Zinneerah ya dawo gida. Dan Abba ya sanarma Baffah cewar wancan zuwan da yayi ya iske bayanan ya bar gari ba'asan inda yakeba.
A take maigari ya aika kiran Baba da su Kawu Rabilu, shi kuma ya shiga gida yasa aka fara haɗa fura da sauran cimar ƙauye domin fitoma baƙi. Bayan ya aika a siyo musu ruwan leda da lemo acan kusada dan musamman ya tada mai mashin.
★★
Baba na ƙofar gida tare da ƴan uwansa yana basu labarin tun barinsa gida ashe Niger ya dosa, acan yayi gamo da wani bawan ALLAH daya taimakesa saboda fahimtar baya cikin hayyacinsa da yayi. Shine ya dage masa da addu'a da neman magani harya samu lafiya acikin watanni shida. Koda yaga ya warke duk da ya tuna komai daya faru sai yace bazai dawo gidaba zaiyi zamansa can neman arziƙinsa. Aiko wannan mutumi yaji daɗin haka. a take ya ɗaurasa akan hanyar sana'a, cikin ƙanƙanin lokaci ALLAH ya amince masa abubuwa suka canja ya fara juya kuɗaɗe duk da bawai masu ɗunbin yawaba. Nadai rufin asirin ALLAH dai-dai gwargwado. Ganin zaman nasa bana ƙare bane mutumin daya taimakesa ya bashi auren ƙanwarsa da mijinta ya rasu bakuma ta taɓa haihuwaba, hasalima shekarunta biyar kacal dayin aure. Ya amsa hannu biyu yayma ALLAH godiya da wannan bawan ALLAHn nan, ya kumayi sa'a Zainaba nasonsa itama. cikin amincin ALLAH basu rufa wata uku ba sai gata da ciki, sunyi murna sunyi farin ciki mara musaltuwa. Da cikin ya tsufane yaga ya dace yazo gida da ita ta haihu a cikin danginsa, shine dalilinsa na ɗakkota suka taho yanzun.
Cikin jin daɗi Kawu Sabi'u yace, “Yaya to yanzu kadawo garemu baki ɗaya kokuwa haihuwa kawai aka kawo yayarmu tayi ka sake gudu ka barmu?”.
Kafin Baba ya bashi amsane ɗan aiken maigari ya iso. Tun anan ya gumtsa musu zancen baƙi. Cike da mamaki suka tashi suka bisa dan su dukansu fes suke cikin shiga ta kamala babu wani damuwa.
Lokacin dasu baba suka iso sun iske an cikama su AK gaba da kayan abinci, duk da dai fura ce da ruwa da lemo, sai zabi da maigari yasa aketa yankawa ana shiga dasu cikin gida dan yacema matansa dan ALLAH suyi maza a gyara a gasasu gashi mai ƙyau.
Fahimtar muhimmancin baƙin ya sakasu miƙewa suma babu sanya suka haɗu da ƴaƴansu suka fara aikin babu wasa. Koda su Baba suka iso Baffah ya buƙaci su zauna a waje suyi magana iyakarsu manyan. Sanin maganace mai muhimci tafe dasu maigari yasa aka sake saka musu tabarma ƙatuwa a zaurensa na biyu dake ƙarami bai kai na farko girmaba.
Bayan duk sun zauna sukai gaisuwa ta mutunta juna. Inda Abba ya bama baba sani. Baba da dama tuni yake masa kallon sani yace, “Haba koda naji, tun ɗazun naketa tunanin wannan fuskar kamar na santa amma na kasa. Kai sannunku da zuwa, sannunku”.
Fuskar Abba da murmushi yace, “Yauwa mun gode sosai Malam Sulaiman. Nasan zakai mamakin wannan zuwa namu, sai dai ba abin mamaki baneba. Kwanaki nazo garin nan amma ban samekaba. Zuwan nawa kuma yanada nasabane da Zinneerah ”.
Da sauri baba ya dubesa jin sunan gudan jininsa abar begensa a koda yaushe. Murya a raunane yace, “Zinneerah kuma Alhaji Abubakar? Ai ina mai baƙin cikin sanar dakai muma nemanta mukeyi tun bayan wani babban al'amari na ƙaddara daya giftama rayuwarta”.
“Eh nasan duk wannan Malam Sulaiman, dan akansama nazo kwanaki, sai dai rashin samunka ya sani komawa. Yanzu dai a taƙaice Zinneerah tana tare damu, dan waɗanan bayin ALLAH daka ganni tare dasu ma a dalilinta sukazo nan. Wannan” ya nuna Baffah. “Shima kawuntane, dan yayane ga hauwa'u, nasan dai bazaka gaza jin labarin dangin mahaifiyarta dake a bauchi ba sanda kuna tare? To Alhaji Kabir Shira yana ɗaya daga cikinsu, sannan kuma yaron wajensa ne ke son auren ita Zinneerah shiyyasa mukazo nan”.
Wani irin daɗi da al'ajabine ya bayyana a fuskokin su Baba da maigari da su Kawu Rabilu. Baba da ƙwalla suka cikama ido yace, “Ashe dama Zinneerah na tare daku? Kai ALLAH na gode maka da wannan ni'ima taka. Nagode maka ALLAH daka bama yarinyata kariya ta hanyar sadata da mahaifiyarta. Sannan kuma nagode muku da kuka zama masu karamci daƙin riƙe baya a ranku kuka jiƙan gudan jinina duk da hanaku ita danai a lokacin da kuka buƙata. Kuyi haƙuri, bansan da wane irin yare ko harshe zan muku bayaniba, amma tunda ba wannan ya taramu yanzuba mu fara maganar da kukazo da ita, waccan zata biyo baya danni na cancanci naje inda kuke muyita. Batun auren Zinneerah kuwa wlhy koda bakuzo inda nakeba kunada iko da damar aurar da ita ga duk wanda zuciyarku ta baku yarda akan ingancinsa da mutuncinsa. Dan haka ni dai a ɓangarena babu matsala na bama wannan yaro Zinneerah halak malak. Ga kuma ƴan uwana nan inada tabbacin bakinmu ɗaya dasu”.
Cikin jin daɗi da farin cikin kalaman baba su Baffah suketa ambaton Alhmdllh bakunansu a washe. Alhaji Yusif yace, “Masha ALLAH, gaskiya munji daɗin wannan karamci, sai dai kuma muna roƙon alfarma ta biyu idan bamu takura muku ba”.
Kawu Sabi'u dake kusa dashi yace, “Alhaji ku ɗauka mudaku duk ɗayane, dan koba komai kuma kunada ƙarfin iko akan Zinneerah, dan haka ba zancen alfarma a tsakaninmu”.
Nanma kowa ya nuna jin daɗinsa. dan haka kai tsaye Alhaji Yusif ya sake faɗin, “To Alhmdllh, dama alfarmar tamu dai bata wuce cewar mufa da shirinmu mukazo nan ba, ma'ana da shirin ɗaura aurenma baki ɗaya muka iso bawai tambaya ba. Muna buƙatar ɗaurin auren ne a gaggauce bisa wani dalili da insha ALLAH daga baya za'a tattaunashi. Fatanmu dai a ɗaura auren kawai”.
Duk da baba yaji daɗin wannan zance sai da yay ɗan jimmm, kafin ya gyara zamansa murya a sanyaye yace, “Amma Alhaji dakun bari dai a fara magana ta fahimta, dan yadace ace kunsan ƙaddarar data afkama yarinyar nan harta kai ga barin gida ta iskeku”.
Da sauri Baffah yace, “Karka damu ɗan uwa, duk abinda kake ƙoƙarin son sanar mana mun sanshi, dalilin sanin nema yasamu cewa a gaggauta ɗaura auren yau, daga baya dukma abinda zai biyo baya sai ya biyo”.
Daɗine sosai ya ƙara kama baba, cikin share ƙwalla yace, “Shikenan mun amince, dan haka ga ƴan uwana nan suke da sauran magana”.
Kowa ya nuna farin cikinsa ananma. Dan haka maigari ya fita cike da farin ciki ya sanarma sanƙira a sanar da ɗaurin aure yanzu idan anyi salla a masallacin juma'a.
Cikin ƙanƙanin lokaci sanarwar sanƙira ta gauraye ƙauyen danya. Kasancewar dama azhar ta taho nan mutane suka fara haramar nufar massalacin juma'a domin yin salla duk da ba juma'ar baceba. Suma su AK da duk basusan mi ake cikiba fitowa sukai sukayi alwala. Mutane sai kallonsu suke tamkar sun sami television. Yara kuwa nata kaima mata labari a cikin gida.
Koda suka shiga cikin massallacin liman sai yaja baya, a mamakin kowa sai gani sukai ya kamo hannun AK ya tsayar a mazaunin liamami.
Kasa magana AK yayi ya tsaresa da idanu, ganin yanda yayi ɗin sai Liman yay murmushi, kansa tsaye yace, “Kai kafi cancanta da ka jamu salla badan nasan kaiɗin wanene ba. Haka kawai zuciyata ta rayamin baka wannan damar, dan haka dan ALLAH karkai musu ko jayayya”.
Baki AK ya buɗe zaiyi magana Baffah ya girgiza masa kai alamar yabi umarni kawai. Dole ya ɓame bakinsa yana wani lumshe idanu da buɗewa a lokaci ɗaya. Dolensa ya juya yana gyara taiwarsa, a ransa rayawa yake da ace baida ilimin addini lallai yau da yaji kunya mai tsanani ashe.
(hummm, jama'a ni kaina sai da na sauke numfashi saboda jin muryar Abdul-Mutallab Kabir Abdul-Mutallab shira dake raira karatu a nutse a cikin salla, dan yanda yake cikin masu jajayen kunne banyi zaton yanada ilimin addini haka ba).
Kasancewar ƙaramin gari jin baƙuwar murya da salon karatun yasaka mata cece kucen anyi baƙon balarabe mai jan salla yau a babban masallaci, a cikin wannan zantuka kuwa hardasu yaya Gajeje dake zagaye da Inna dake kwance rijib babu lafiya tun faɗuwar jiya, da alama dai hawan jini ne ke neman bigeta.
A masallaci kam bayan an idar da salla aka tsaida mutane duk da kuwa dama sunsan da zancen ɗaurin aure da aka sanar dan shine maƙasudin taruwarsu da yawa haka a massallacin tunda akwai kananun masallatai.
Mamakine ya kama su AK jin alinahin liman na sake sanar da maganar ɗaurin aure. AK ya kalli Baffah cike da alamomin tambaya, wani murmushin manya Baffa ya sakarma AK ɗin yana ɗauke kansa ya maida ga Haneef. Magana ya faɗa masa a kunne. A take Haneef ya tashi yana jan hanun Mas'ood suka fita. Cikin mintuna ƙalilan suka dawo da yara ɗauke da kwalayen sweets da huhunan goro da biscuits. Bayan an ajiyesu Alhaji Mansur ya ciro kuɗi ƴan dubu-dubu sabbi ƙal ɗauri biyu ya ajiye a tsakkiyarsu alamar dai kuɗin sadaki ne.
Kai Kawu Sabi'u ya girgiza da faɗin, “Alhaji sunyi yawa, dubu ashirin sun isa matsayin sadaki”.
Baffah ne yay murmushi shima yana girgiza nasa kan. yace, “Darajar ɗiyata ta wuce dubu ashirin, idan tanima za'abi sai sun ƙara mana sadaki wannan yayi kaɗan”.
Kusan waɗanda ke a kusa dasu sai da suka zaro idanun mamaki, Baba yay saurin faɗin, “A'a dan ALLAH ayi haƙuri alhaji, waɗanan ɗinma sunyi yawa kamar yanda Sabi'u ya faɗa”.
“Basuyiba malam Sulaiman”. Cewar Alhaji Yusif. Abba ma yay murmushi da kallon Baba. “Kamar yanda Alhaji Kabeer ya faɗa a barsa haka ɗin kawai ALLAH ya sanya albarka ya basu zaman lafiya da zuri'a ɗayyaba”.
A take aka amsa da amin, tare da shiga hidinar ɗaurin aure kai tsaye. Bayan tsarebe-tsaraben ɗaurin aure da addu'a. Sanƙira ya miƙe ya fara shelantawa ga jama'a an ɗaura auren *_“Alhaji Abdul-Mutallab shira da amaryarsa Zinneerah Sule baduku akan sadaki naira na gugar naira, wuri na dukan wuri dubu ɗari biyu”_*...............✍
*_Tofa, yaufa ake ƙuru-ƙuru, jama'a yaya wannan labari zai kasance a kunnen hajiya aunty mandiya gimbiya Farah uwargida ran gida a gidan Abdul-Mutallab shira. Yaya kuma Mammah zataji? Sai kuma uwar gayya Zinneerah da batasan hawaba batasan saukaba. Shin yaya takene a zuciyar mai gayya mai aiki Abdul-Mutallab Kabir Shira? Moos'ab, Khalipha yaya zasuji da wannan juyin mulki?. Inna dake iƙirarin Zinneerah na birnin ikko yaya zataji?. Amsarku duk tana acigaban MAKAUNIYAR ƘADDARA da nakeda tabbacin yazo muku da sabon salo na musamman 🤏🏻🤓, kumuje zuwa yanzu aka fara wasan_*
_Asha hutun weekend lafiya😍😘😍😋💃🏻💃_.
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 41*
_________________________
*MG'S SKINCARE*
Hi my peole🙋♀️
Are you tired of using different skincare product that won't work on ur skin no matter what❓then trust me @mg's skincare is the right plug for you💯
Are you guys battling with pimples,dark spot, sunburn, acne, stretch mark,knuckle,dark armpit,damaged/bleached skin
Have you getting dark due to childbirth or sun exposure🥺worry no more@mg's skincare gat you covered✅
Want ur skin to glow buh you don't like using cream/lotion try *mg's herbal whitening black soap* nd you'll achieve that free/shiny skin🧚🏻♀️
For those that wanna achieve that milky flawless skin that turns head wherever you go🧚🏻♀️ try mg's *beauty kit* that's the secret to beautiful skin😎you'll get an amazing magic result😘 you can also buy the soap nd combine it with any of our product to get more result😀
Glow gang
What are you waiting for
Shop urs now before we get sold out again😍
Mg's product is 1in town😃if you know you know kawai😜
Nd mg's products are organic they dnt bleach they are made with natural ingredients that will make ur skin lk brighter nd tone ur skin😘 it just bring out that hidden beauty in you😘we HV everything available now so is time to glow dearies
Pamper ur skin🧖♀️
Shine like a bride💯
Make ur skin brighter🤗
Glow🦵
Soap price:3k
Beauty kit:11k
Chat 08062991549
Call 08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
DNT forget to follow us😇like/comment😍
Team glow🤝
_________________________
*Page 41*
............Tun farkon fara ƙulla auren da yaji sunansa a ciki yay mutuwar zaune, bai dawo hayyasa ba sai da sanƙira ya ƙara tabbatarwa da babbar murya. A hankali AK ya lumshe idanunsa dake ɗauke da nauye-nauye kala-kala a cikinsu yana sauke wata ɓoyayyar ajiyar zuciya.
Haɗa ido sukai da Baffah dake masa kallon nazari, kansa ya maida ƙasa yana ƙoƙarin danne ɓoyayyan al'amarin dake neman bayyana kansa a saman fuskarsa. Shima Baffa sai kawai ya ɗauke kansa zuciyarsa na masa wasiwasi.
Koda aka mimmƙe domin fita a masallacin da ƙyar Saifudden ya iya kama Moos'ab da yay suman zaune, dan tun farkon fara ƙulla auren da yaji an ambaci Yayan nasu sai da gabansa ya faɗi, jin zancen sanƙira kuwa tamkar saukar guduma ne a bisa tsakkiyar kansa. Gefe Saifudden ya maida shi tare bashi ruwa dan yasha. Babu musu Moos'ab dake hawaye kamar wani mace ya amsa ya sha ruwan yana sauke tagwayen ajiyar zuciya.
“Wannan shine abinda na gudar maka tun farko Moos'ab, shiyyasa nace ka bayyanama Zinneerah kana sonta, ka kuma sanarma Baffah da Granny amma kaƙi wai saita gama secondary school, gashi nan to shi Yayanmu yayi wuff da ita”.
Murmushi mai ciwo Moos'ab yayi, cikin raunin murya yace, “Saifudden ALLAH ya ƙaddara dama shine mijinta, kuma ni wlhy na haƙura na bar masa har abada. Yayanmu yanada daraja da mutuncin da zamu iya sadaukar masa da komai, komai muhimmancin abinnan kuwa. Dan shima yayi mana abubuwa masu ɗunbin yawa da bazasu ƙirguba. Sannan nasan Zinneerah zata samu dukan farin ciki daga garesa insha ALLAH. Kuma anyi maganin wannan mahaukaciyar matar tasa da kishi ya maida zararriya, wlhy kodan kiran dataimin jiya da dare wai saina faɗa mata uwar little yasa naji daɗin ƙulla wannan auren, tunda tana kukan targaɗe ga karayanan ta samu, sai tai zaman jinya kuma”.
Rungumesa Saifudden yayi yana share ƙwalla shima. Ya ɗagosa yana share masa hawaye da faɗin, “Naji daɗin kalamanka Moos'ab, hakan kuma ya tabbatar min yaƙin da Granny da Baffa keyi akan sanin darajar zumincinmu ba abanza sukeyiba. Tabbas Yayanmu ya cancanci sadaukarwar da tafi haka ma, inaji a jikina kuma maganar shekaran jiyace ta kawo wannan ƙulla auren, amma tabbas sun dace wlhy”.
“Tabbas na yarda da zancenka Saifu. Da alama hauka tai musu na haƙiƙa shiyyasa Yayanmu da Baffah suka yanke wannan hukuncin, na taya Yayanmu murnar samun nutsatstsiyar yarinya mai kunya da tarbiyya ga haƙuri, sannan itama na tayata murnar samun gwarzon namiji mai haƙuri da mutunci, uwa uba ya tara qualities masu yawa da duk mace take buƙata ga mijin aure, duk da nasan akwai ta inda shima yake da rauni kodan kasancewarsa ɗan adam kamar kowa. ALLAH ya basu zaman lafiya, yasa ta zama sanadin farin cikinsa da kwaranyewar hawayensa akan rashin haihuwa”.
“Amin ya rabbi” Saifudden ya faɗa yana sake rungumesa.
A hankali AK dake a bayansu basu saniba ya ɗanja da baya yana lumshe idanu, tun sanda Saifudden ya kamo Moos'ab suka fito ya biyosu, dan ya jima yana zargin akwai wani abu tsakanin Moos'ab da yarinyar, ashe kuwa da gaskene. Hannu yakai bisa sajensa ya ɗan shafa, kafin ya bar wajen batare da ya bari sun gansaba.
Moos'ab ne ya farga da ƙamshin turarensa. Yaɗan janye Saifudden yana faɗin, “Bro ƙamshin turaren Yayanmu fa kamar nakeji”.
Saurin ja baya Saifudden yayi shima yana waige-waige, sai dai basuga kowaba a wajen, “Inaga hancin kane kawai, kaga zomuje karma a nememu”.
Koda AK yabar wajensu nufar inda su Dr Mahmud suke yayi, inda ya samu wani maroƙi yanata zabgama masa kirari duk zatonsa shine angon. Yana ganin AK ya iso ko yay saurin kamo hannunsa da nuna musu shi, “Yauwa to ga angon nan bayin ALLAH”. Ya faɗa yana ciro kuɗi ya miƙa musu yana tura AK gabansu yana dariya.
Idanu sosai AK ya waro waje ganin sun zagayesa suna masa ihu akai, ai gudun hayaniyar tasu ya sashi babu shiri ciro kuɗi ya miƙa musu yana harar Dr Mahmud daya koma gefe yana kwasar dariyar mugunta, su Mas'ood na tayashi ƙasa-ƙasa.
Jama'ar gari kuwa ganin ango yasa suketa sake tofa albarkacin bakinsu. Wasu suce ita cikin shege ya mata riba, wasu suce koma shine abokin tsiyar tata, wasu su tayata murna, wasu suce sakkayar ALLAH ce ga zalincin da Inna tai mata, wasu suce baisan ta taɓa yin cikiba ƙila data bar garin ta zubar ne. Wasu ko hassadace kawai, kasancewar sunso zinneerah ɗin basu samuba. Magana dai iri-iri. Har takai wani ya samu AK gefe yana masa gulmar wai kuwa yasan waya aura?.
AK dake jingine jikin mota yana latsa waya ya ɗago ya dubi mutumin ƴar walwalar fuskarsa na ɓacewa ɓat. Amma duk da haka mutumin nan sai yay ƙasa da kai yana wani soshe-soshe. “Ayi haƙuri Alhaji, ganinka mutum mai tarin kamala da mutunci yasa naji bara na faɗa maka gaskiya, dan na tabbatar an rufekane akan yarinyarnan. Duk da kafin faruwar komai kowa yasan yarinyar kirki ce a garin nan dan har kwatance akema yara akanta. Amma daga ƙarshe ta ɓata rawarta da taalle. Dan kuwa cikin shege tayi, Katsina tabi saurayi sukayo kusan mako biyar sannan suka dawo, a dalilin cikinne ma ta gudu a ƙauyen nan babu wanda ya sake jin labarinta sai yau da kukazo wai aurenta. Nifa k........”
Wani shegen kallo da AK ya dasa masa dai-dai ya ɗago ya sashi saurin haɗiye sauran zancen yana zazzare ido. AK ya gyara tsaiwarsa idanunsa na canja launin ɓacin rai, cikin nutsuwarsa da rashin sakewa yace, “To dakazo kana faɗamin idan kuma nine nayi cikin fa?”.
A razane mutumin ya waro idanu waje. Sai kuma yay saurin yin ƙasa da kansa yana girgizawa. “Haba-haba Alhaji ni nasan hakanma bazata faruba. Ai daga ganinka anga mutum mai mutunci da kamun kai, kawai dai an rufekane, amma dan ALLAH karka bari so ya rufe maka ido ka ɗaukama ƴaƴanka uwar banza”.
“Ai kaine banzan sha-sha-sha” AK ya faɗa a fusace, cikin kaushin murya yace, “Mutumin banza kawai, saboda tsabar rashin mutunci ko kunya bakajiba kai kazo kana aibantamin mata? To bara na sanar maka kaima kaje ka sanar tunda naga shine aikinka. Shi wannan cikin da kuka ganta dashi nawane. Nine nai mata kuma ta haifamin, daɗin hakannema yasa na aureta yanzu stupid ɓacemin anan”.
Da sauri mutum yabar wajen kuwa tamkar zai kifa, AK ya rakashi da wani irin kallon tsana da takaici, tsabar takaici dole ya buɗe motar da yake a jingine ya shiga batare daya rufe murfinba ƙafafunsa a waje. Sosai launin idanunsa suka sake canjawa, badan kar ace yayi ƙarantaba da lallai saiya nunama shegen mutumin nan kuskurensa yau wlhy. Tsaki yaja da dafe kansa dahar ya fara masa ciwo ƙasa-ƙasa zuciyarsa na masa zugi. Tabbas yanada buƙatar dawowa ƙauyen nan domin wanke yarinyarnan duk da har yanzu baisan yaya ya samar da Abdul-Mutallab ba.....
“Yayanmu!” Moos'ab ya sake kiran sunansa a karo na uku.
Sai yanzu kunnensa ya ji, ɗago idanunsa yay ya dubesa, Moos'ab yay ƙasa da kansa cikin girmamawa yace, “Baffah ke kiranka”.
Komai baicema Moos'ab ɗinba ya fito a motar ya nufi cikin zauren maigari inda su Baffah suke tattaunawa da Baba akan abinda suka sani game da ƙaddarar data afkama Zinneerah da har yau basusan mafarintaba.
Waje ya samu ya zauna yana ƙoƙarin ɓoye ɓacin rai da takaicin da mutumin can ya cusa masa. Cikin girmamawa ya sake gaida su Baba dan yanzu dai a matsayin suruki yake. Sosai baba yaji daɗin wannan girmamawa. yakumaji a ransa AK ya kwanta masa, yana taya ƴarsa murna dajin insha ALLAH ta samu mijin marainiya.
A nutse baba ya sake maimaita masa bayanin da yayma su Baffah game da Zinneerah, sannan a ƙarshe ya roƙesa alfarmar dawowar Zinneerah danya domin shirya mata biki nanda wata ɗaya.
Ɗan murmushi AK yayi kansa a sunkuye yace, “Baba karka damu, duk yanda kukaso muyi mu masu biyayyane a gareku, sai dai kayi haƙuri a yanzu bata ƙasar tana can London, insha ALLAH nan da sati biyu zata dawo”.
Cikin ɗan waro ido Kawu Rabilu yace, “Landan kuma? Ita Zinni ɗin?”.
Sosai yanda Kawu Rabilu yayi ya basu Saifudden dariya. duk sukai ƙasa dakai suna gumtse bakuna. Baffah ne ya amsama kawu Rabilu da cewar, “Eh suna can gidansa tare da mahaifiyata da taje ganin likita. Amma kamar yanda ya faɗa insha ALLAH nanda sati biyu zasu dawo, kuma insha ALLAH suna dawowa zata dawo nan ɗin itama a ɗauketa kamar kowace ƴa a kaita gidan aurenta”.
Jinjina kawuna suka shigayi na gamsuwa. Yayinda bakin Baba da nasu Kawu ya kasa rufuwa. Kasancewar yamma tayi sukai haramar tafiya. Naman zabi da basuciba haka maigari yasa aka saka musu a mota hardasu tsarabar mangwaro, gwaba, kashu da nono da ƙwan zabbi. dan su Baba suma sai gasu da nasu tsarabar harda Gwaggo Laritu da labari ya kaima ta bakin ƴaƴanta.
Lokacin da zasu wuce haka jama'a suka zagaye motocinsu anata ɗaga musu hannu. Sosai su Baffah sukaji daɗin wannan karamci, dan haka suka tafi zukatansu fes kowa na ALLAH ya sanya alkairi.
★★★
Tun kafin Baba ya shigo gida labari ya samu su Inna. Zaune ta tashi dangangan kamar ba itace kwance kashirɓan tana kukan ciwo da ɗan nishi ba. Cikin masifa take cema mai kawo labarin, “Kukam dai annamimanci bai muku kaɗan abaki Sahware. In banda shegen munahinci yaushe kikaga wata Zinni da har za'a ɗaurama aure. Dalla hice mani agida kahin nai miki bankaɗa wlhy”.
Baki Safare ta taɓe tana faɗin, “To oho ni dai Asabe. Koki yarda ko karki yarda yanzu na wuto ana ɗaura auren Zinni a masallacin juma'a. Banga dalilin da zaisa nazo na hiɗi abinda bashike nanba”.
“Kai kedai Sahwar ALLAH ya tsine maki albarka bankaɗaɗɗiyar mata watsatstsiya. Ki hitamin a gida wlhy kona nafka maki shegen duka naga mai ƙwatarki”.
Fita Safare tayi tana wata shegiyar dariya. Ana haka kuwa sai ga Tinene ta shigo gidan a guje tana hakki.
“Ke kuma lahiya kika shigoma mutane kamar wata korarra?”.
Yaya Gajeje ta faɗa dan shigowarta kenan gidan ko zancen Safare batajiba.
Cikin hakki Tinene ta dafe kanta dake mata ciwo dan dama sayan paracetamol ta fita yi, tace, “Inafa lahiya Yaya Gajeje. wlhy wani labari najiyo yanzun. ga baba can a babban massallaci an ɗaura auren Zinni da wasu mutane manyan ƴan gayu al-qur'an”.
Tsit gidan yayi na wucin gadi, sai da Sa'a tace, “Inna anya kuwa maganarnan bada gaske bane? Bara dai na hita nima na jiyo mana”.
Yaya gajeje da sai yanzu taji abinda ke faruwa cike da zumuɗi tace, “Jeki jeki maza Sa'a. Kai ALLAH ya tabbatar da wannan zance da nayi hwarin ciki mara misali wlhy”.
Amaryar Baba da duk ke saurarensu tun ɗazun bata tsoma bakiba ta kalli Yaya Gajeje da cewa, “Wacece wai ita Zinni ɗin?”.
Kai tsaye Yaya Gajeje dake murmushi tace, “Ƙanwarmuce itama mama........”
A fusace Inna ta zaburo tana watsama Yaya Gajeje harara, “Ƙanwarku a gidan ubanwa. Gajeje ki kiyayeni. Ke kuma munahika da kike tambaya bara a faɗa miki, itana ƴar kishiyace da zaman gidan nan ya gagareta kamar yanda kema zai gagareki. Dan wlhy na ɗau alwashin yanda na watseta kema saina watseki a gidan nan dama garin nan baki ɗaya”.
Murmushi amarya tayi tana ɗauke kanta batare datacema Inna komai ba. Hakan kuwa ba ƙaramin harzuƙa zuciyar Inna yayiba. Ta miƙe dingangan kamar ba ita ke ciwo ba tahau zazzaga bala'i tana zagin amarya da mmn sadiq da Zinneerah. A wannan bala'in baba ya shigo shi dasu kawu da yara ɗauke da kayan sweets dasu biscuits da huhunan goro cikin gidan. Suna shigowa Gwaggo Laritu ma na shigowa.........
★★★★
A ɓangaren su Baffah kam tunda suka bar Danya kowa ke tattauna karamcin da akai musu da abokin tafiyarsa. Motar su AK ce kawai ta kasance shiru dan tunda suka tafi ya jingina kansa da kujera ya lumshe idanu yana tariyo maganar mutumin nan ma ɗazu daki-daki cikin ransa. Lokaci-lokaci Dr Mahmud kan kallesa yayi murmushi. Sai da suka kusa shiga cikin kano ne ya ɗan sake dubansa da tsokana, “Haba ango duk daɗine ya saka zama kurman ƙarfi da yaji?”.
Shiru AK bai motsaba, sai da ya mula dan kansa ya ɗan buɗe ido ya harari Dr Mahmud ɗin, cikin rashin sakewarsa yace, “Dama haka kake da sa ido?”.
Dariya sosai ta kama Dr Mahmud har yana dukan sitiyari. Hakan ya saka AK ɗan sakin murmushi ya maida kansa ya sake kwantarwa da lumshe idanu. daga nan bai ƙara tankawa Dr Mahmud ɗinba daya cigaba da tsokanarsa har suka isa gida.
Sun iso suka iske hajiya Bilkisu da suke kira da Mommy ta iso tare da babban ɗanta Huzaifa. Huzaifa kusan sa'an AK ne, sai dai AK ya girmesa da kusan shekara biyu, amma ayanzu abokaine, dan saima suna tsokanar junane zaka iya sanin AK ɗin ya girmi Huzaifa.
Dr Mahmud na ajiyesa bai shigaba ya juya gida danya huta shima. Hakan yasa AK nufar sashen Hajiya Iya shi kaɗai, su Haneef kuwa duk sashen iyayensu sukai kai rahoton ɗaurin aure. Hakama Baffah ɗokin jin zuwan ƴar uwarsa yasashi nufar sashen nasa kai tsaye dan tanacan, tunda bada yara tazo ba duka bazata sauka a nata sashen ba.
Tunda AK ya shigo yaga Huzaifa zaune a falon Hajiya iya yanacin abinci sai ya ɓata rai cikin ɗan wasan da suka saba yace, “Oh oh yaushe wannan bawan yazo mana gida” ya faɗa yana harar Huzaifa.
Dariya Huzaifa ya fashe da ita, saida yayi mai isarsa ya haɗe fuska yana harar AK ɗin shima. “Eh lallai ka nunamin kayi aure na biyu, ninema Bawan naka? Yaro jeka bincika ni dakai wanene bawa?”.
Hannu AK yasa ya tallare ƙeyar Huzaifan. Yay gaba da sauri yana faɗin, “Magananne jeka bincika kaidai”. Ya faɗa yana shigewa ɗakinsa murmushi ɗauke akan fuskarsa. Dan inhar yana tare da Huzaifa kobaiyi niyyar fara'a ba sai ya sakashi yinta dole saboda shi mutumne mai barkwanci dason wasa.
Cikin ihu Huzaifa yace, “Jeka fito ka sameni mijin mata biyu, indai maganace kuwa ka haɗu da ita yau ko barci bazan barka kayiba”.
AK na jiyosa daga ɗakin, dan haka ya girgiza kansa kawai yana murmushi. Kayan jikinsa ya cire ya nufi toilet dan watsa ruwa a gaggauce lokacin sallar magrib karya ƙure masa.
★★
Abba kam koda ya isa gida da albishir ɗin ɗaura auren Zinneerah da AK ga Mmn sadiq sai kawai ta fashe da kuka dan farin ciki, Abba dake mata dariya ya rungumeta yana lallashi.
“Tabbas mutanen nan sun cancanci yabo Hauwa'u. Dan halayyarsu na mana nuni da cewar har yanzu akwai mutanen ƙwari masu mutunci da sanin yakamata a cikin masu arziƙi bakamar yanda mu mutane muke zargiba. Inda ace ana samu mutane irinsu Alhaji Kabeer Shira koda a talakawanma wlhy da duniya ta zauna lafiya. Amma yanzu zakiga kowa ɗansa kawai da mutuncinsa yake karewa. Babu ruwansa dabin gaskiya koda ace yana ganinta ƙuru-ƙuru kuwa. Sau da yawa akan ɓata tarbiyyar yarinya amma kiji iyayen yaron na amabaton ɗansu bazai auri lalatacciya ba. Bayan kuma bata lalaceba sai da taimakon ɗan nasu. Tare suka aikatafa, amma sai a nuna tsangwamar macen fiye dashi namijin dan son zuciya. Bayan kuma shi namijin yafi macen hankali, ko ya girmeta, maybe ma shine yay amfani da wayonmu na maza ya lalata mata rayuwar tata. Hakan zaluncine dason zukata muke aikatawa wajen ƙasƙantar da mace akan zunubi koda kuwa tare ta aikatashi da abokin halittarta namiji.”
Hawaye mmn sadiq ta share tana duban mijin nata, “Yaya ai mutanen duniya haka suke tun na ƙarnin farko, suna amfani da raunin ɗiya mace akoda yaushe wajen sake raunanata, sun mance a ɓangaren zunubi da hukunci duk iri ɗaya UBANGIJI zai mana ga duk wanda ya saɓa masa. Wlhy bammasan yanda zan musalta maka daraja da kima ta mutanen nanba a zuciya ta, sukam waɗanne irin mutanene haka masu tarin adalci da sanin darajar ɗan adam?”.
Cikin dariyar farin ciki Abba yace, “Tabbas sun cika ƴan baiwa, dan samun irinsu a cikin al'ummarmu sai an tona. Amma akwaisufa. Yawaitar masu son zuciyarne ya lulluɓe irinsu saboda ƙarancinsu a cikin mutane. ALLAH ya bamu ikon koyi dasu”.
“Amin” mmn sadiq ta faɗa wani irin sanyi da nutsuwa na saukar mata lokaci guda.
Abba yace, “Yauwa inaga ki shirya Abdul-Mutallab zasu aiko a ɗaukesa daga can gidan wai ƙanwar Alhaji Kabeer ɗince zatazo daga Lagos yau, itama za'a kaimata shi ta gansa”.
Kai mmn sadiq ta jinjina masa tana faɗin, “To bara ka gani naje na tadashi a barci can kuwa sai nai masa wanka basai sunzo sunyi zaman jiraba”.
Cikin gamsuwa da bayaninta ya kaɗa mata kai..........✍
_Kuyi manage da wannan an mana rasuwane ban samu zaman nustuwar typing ba😊🙏🏻_.
*_A page na ƙarshe na ranar Friday akwai inda nai kuskure, hakan ta farune dalilin rashin yin editin ranar, nayi typing na gaji. Inda nasa AK yayi limancin sallar zuhur nayi maganar yayi karatun salla har mutane na ambaton anyi baƙon balaraben limami. Please amin afuwa. Wannan ajizancine na ɗan adam sai daga baya na farga dalilin maganar da wata tayi na sake komawa na duba page ɗin. Ina ƙara bada haƙuri Please, mantuwa ce da rashin editin kamar yanda na faɗa tun farko😊🙏🏻_*
*Barkanmu da dawowa hutun weekend😍😍😘😘😘💃🏻*
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
*Page 42*
_________________________
*MG'S SKINCARE*
Hi my peole🙋♀️
Are you tired of using different skincare product that won't work on ur skin no matter what❓then trust me @mg's skincare is the right plug for you💯
Are you guys battling with pimples,dark spot, sunburn, acne, stretch mark,knuckle,dark armpit,damaged/bleached skin
Have you getting dark due to childbirth or sun exposure🥺worry no more@mg's skincare gat you covered✅
Want ur skin to glow buh you don't like using cream/lotion try *mg's herbal whitening black soap* nd you'll achieve that free/shiny skin🧚🏻♀️
For those that wanna achieve that milky flawless skin that turns head wherever you go🧚🏻♀️ try mg's *beauty kit* that's the secret to beautiful skin😎you'll get an amazing magic result😘 you can also buy the soap nd combine it with any of our product to get more result😀
Glow gang
What are you waiting for
Shop urs now before we get sold out again😍
Mg's product is 1in town😃if you know you know kawai😜
Nd mg's products are organic they dnt bleach they are made with natural ingredients that will make ur skin lk brighter nd tone ur skin😘 it just bring out that hidden beauty in you😘we HV everything available now so is time to glow dearies
Pamper ur skin🧖♀️
Shine like a bride💯
Make ur skin brighter🤗
Glow🦵
Soap price:3k
Beauty kit:11k
Chat 08062991549
Call 08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
DNT forget to follow us😇like/comment😍
Team glow🤝
_________________________
*Page 42*
...........Cikin farin ciki Baffah da ƙanwarsa Mommy (Bilkisu) suka tari juna, duk da kuwa basu daɗe da rabuwa a london ba duba mahaifiyarsu Hajiya iya. Sama-sama suka gaisa ya shiga ciki watsa ruwa. Koda ya fito massallaci suka fice da matasan ƴaƴansa. Sai da aka idar da sallar isha'i sannan suka sake shigowa gidan.
Sai lokacin matan gidan suka sami damar zuwa masa sannu da zuwa da ALLAH ya sanya alkairin ɗaura aure da sukaji a bakin ƴaƴansu.
Hakama Mommy ta shigo har falonsa inda aka shirya musu abinci tare, cikin farin ciki sukaci abinci shi da ƴar uwarsa. Sai da suka kammala suka sami zaman yin hira sosai, inda a cikin hirar ne Baffah yay kiran Khalipha ya sakashi ya haɗasu da Hajiya iya.
Tsaf ya kwashe mata komai ya sanar mata game da ɗaurin aure. Duk da yasan zatai farin ciki dama dajin haka sai yaji murnar data nuna ma ta zarta wadda yay zato, dan albarka dai ya shata har babu adadin ƙididdiga. Suna tsaka da wayarne AK da Huzaifa suka shigo ɗakin. Kai tsaye wajen Mommy data ware masa hannu ya nufa. Ya zauna kusa da ita tare da ɗan hugging ɗinta ta gefe yana murmushi har haƙoransa na bayyana. Dan har ransa yana ƙaunar ƙanwar mahaifin nata saboda itama tana ƙaunarsa.
“Ina cewa zanje na gaisheki tunda wancan zuwan ban samu shigaba sai kuma gaki?”.
Murmushi Mommy tayi dakai hannu ta shafa kan AK mai maganar. Tace, “Ja'iri anya na yarda dakai kuwa? Yanda ka ƙwace mana Inna ka kai London bamma tsammaci zuwanka nan kusaba. Nazata sai bikin su Saffiya, ashe ma kai zaka fara angwancewa kafin su. To ALLAH ya sanya alkairi ya bada zaman lafiya na har abada”.
Kansa ya duƙar yana murmushi, akan laɓɓansa ya amsa da amin.
Cikin tsokana Huzaifa yace, “Aini Mommy soma nake naga wace mai sa'a ce ta shiga tsakkiyar lailah Majnoon ɗin nan haka? Dan naga alamar itama da ƙarfinta take dan tun ɗazun murmushi yaƙi barin fuskar ɗan naki”.
Dariya Mommy da Baffah suka sanya, AK kuma ya zubama Huzaifa harara da masa daƙƙuwa.
Cikin dariya Mommy tace, “To ai kaga ya nuna maka shi ba matsoraci bane, cikakken jarumine tunda gashi har yaje ta biyu, kai kota ɗayanma ka kasa”.
“Faɗa masa dai Mommy. Dan wlhy ban taɓa ganin matsoracin irin wannan yaron ba, maybe sai ya tsufa mu taimaka masa da wata yafendo a dangi”.
Filo Huzaifa ya ɗauka ya jefama AK mai maganar, saurin cafewa AK ɗin yay yana masa gwalo. Su Baffah dai nata musu dariya. Dan kowa yasan dama inhar Huzaifa da AK suka haɗu duk rashin son maganarsa sai ya takura masa yayi harma suyi faɗa.
Suna tsaka da wannan nishaɗin Moos'ab da Haneef suka shigo ɗauke da little daketa faman zuba musu surutun da ba fahinta sukeba sosai suna dariya.
Kusan a tare suka ɗago suna sauke idanunsu akan little. Yayinda Mommy ta sauke wata sassanyar ajiyar zuciya tana kallon yaron ko ƙyaftawa babu da tsarkake sunan ALLAH buwayi gagara misali daya sanya wannan kamar mai ƙarfi tsakaninsa da AK, Huzaifa kuwa hannu ya miƙa masa alamar yazo. Amma sai ya maƙalƙane Haneef yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya.
Haneef ne dake ɗauke dashi ya ajiyesa a tsakkiyar falon yana faɗin, “Bara muga wajenwa zai je”.
Tsit falon yay sunason suga yaya za'a kwashe? Dan yanda little ɗin ke musu kallon ɗaya bayan ɗaya dolene ya baka dariya. Kamar wanda aka raɗamawa sai ya nufi inda Baffah yake, duk zatonsu wajen Baffah ya nufa, dan haka Baffah dake murmushi ya sake gyara zamansa. Yana zuwa gab da shi sai ya zagayeshi ya miƙa hannu zai tsinki appale ɗin dake a jikin flower ɗin kusa da baffan kamarma baiga kowa a falonba.
Hannu baffa ya kai ya dungure ƙeyar little ɗin yana faɗin, “Like father like son” fuskarsa ɗauke da murmushi.
A take duk suka kwashe da dariya, banda AK da yay ƙasa dakai kawai yana murmushi, dan shima dai yanda Little ɗin ya wanu basar da kowa ya bashi mamaki, dan sak halayyarsa na basarwa da mutane ke yawan faɗa masa ya iya.
Hannu Baffah yasa ya ɗaukesa ya ɗaura a cinya yana faɗin, “Ja'iri, saika mana yanga dan kaga muna son ɗaukarka?”.
Kamar little yasan mi baffan ke nufi ya wani ƙyalƙyale da dariyar data basu mamaki, dan sanda suka shigo duk da surutu yakema su Haneef dan zuwa yanzu ya saba dasu fuskarsa a turɓune take.
Suma dai duk dariyar sukayi kafin Baffah ya mikama Mommy shi. Zuciyarta cike da rauni ta amshesa tana murmushi, har cikin ranta jitayi so da ƙaunar yaron na shigarta. musamman yanda yake kamanni sosai da AK kamar yayi kaki ya aje.
Fita su Moos'ab sukayi dan son zuwa su huta. hakanne ya bama su Baffah damar tattaunawa akan zancen little dake lafe jikin Mommy. AK dai baice komaiba. Sai su uku suke maganarsu da juya al'amarin. Ganin sunata jefama AK tambaya a ɗan fakaice Huzaifa yace, “Niko dai zuciyata nason min wani hasashe, amma dai kubari zan sake bincike kafin kuji minene”.
Baffah dake kallonsa yace, “Son faɗa mana mana karka barmu a tunani”.
“A'a Baffah, banson inyi gaggawa ne, amma dai kuyi haƙuri na ƙara nazari akai”.
Haƙura sukai suka barshi akan yayi nazarin. AK da dai dama ba saka baki yake a zancenba sosai ya miƙe yana faɗin, “Bara naje na kwanta wlhy na gani Mommy”.
“Ai ya isa kam agaji Babana. jeka huta kaji”.
“Thanks you Mommy ”. AK ya faɗa yana murmushi da nufar ƙofa. Kamar an tsikari Little dake wasa jikin Huzaifa sai cayay “Abbah zanje”. Danshi kowa Abba ne a wajensa indai namijine babba.
Cak AK ya tsaya tare da juyowa yana kallonsa. shiko da gudu ya sauka a jikin Huzaifa ya nufesa. Babu musu ya kama hannunsa suka fice.
Da kallo duk suka bisu cike da sha'awa, a ransu sunajin tausayin yaron da baijiba bai ganiba, amma yaya zasuyi da ƙaddara kowa da irin tasa. ALLAH ya rubuta cewar ta hanyar daya samar da yaron yaso azurtashi da shi, ya kuma fisu sanin dalilin yin hakan, fatansu kawai ALLAH ya rayashi ya albarkaci rayuwarsa data ƙannensa masu zuwa.
Huzaifa ne ya sake sauke numfashi, hakan yasa su Baffah dawo da kallonsu gareshi, cikin jinjina kai yace, “Ku daina zargin AK ya samar da yaron nan ta hanyar banza. Akwai wani voice recording dana taɓaji a wayar Adilah batare da itama tasan wayar ta naɗa ba, sai dai bai isa zama hujjaba sai nayi bincike”.
Da sauri Mommy tace, “Voice recording kuma akanmi?”.
“Kuyi haƙuri na bincika ɗin zaku sani, kudai ku tayani da addu'a ku kuma bani lokaci”.
Cikin jinjina kai Baffah yace, “Mun baka ɗan albarka. ALLAH yayi jagora muji alkairi”.
Da amin Huzaifa ya amsa yana miƙewa. dan shima so yake yaje ya kwanta ya huta.
________________________★
*_LONDON_*
Ganin yanda Hajiya iya ke murna ya saka Khalipha samun waje ya zauna danta gama ta gumtsa masa. Tana kuwa ajiye wayar ta ɗaga hannu sama tana ambaton Alhmdllh.
Katseta yayi da faɗin, “Niko Granny taƙaita addu'ar nan ki faɗamin minene?”.
Hannu ta sauke tana masa daƙuwa. Sai kuma ta ƙara washe baki da gyara zama. “Burina ne ya cika Abdul-Mutallab ƙarami, ALLAH ya tabbatar da tarkon dana ɗana. Na kuma daɗe ina mafarki da addu'a. Bazan ɓoye makaba yau dama saboda Moddibo nasa aka bani Zinneerah. Dan nasan duk daren daɗewa zaizo ya ganta, ko yasota ko karya sota dama na tanadar masa itane. Sai kuma cikin hukuncin ALLAH ga wani sarƙi ya ɓilla a tsakani........ (tsaf ta kwashe masa labari ta bashi).
Zuciyarsa ce ta shiga tsitstsinkewa, yay saurin yin ƙoƙarin dai-daita yanayin nasa yana haɗiye abinda ke neman toshe fitar numfashinsa. Cikin murmushi da ƴar dariyar yaƙe yace, “Kai kai kai Alhmdllh da wannan daddaɗar labari Granny. Wlhy wannan haɗi yayi kuwa, dan sun dace matuƙa, sannan hakan da baffa yayi shine maganin Aunty Farah da Mammah. Sai dai kuma abinda ya bani mamaki da al'ajabi wai little jinin Yayanmu ne. kainafa ya kulle”.
“Nima nawan a kulle yake Khalipha, amma dai ni yanzu burina jin ta bakin Inno, tunda dai ai ba'a shan ciki a ruwa ko? Sannan kuma babu ta wata hanyar da mace zata samu ciki sai da namiji, dan haka dan ubansu zasuma faɗi yanda akayine su dukansu”.
Ɗan jimm Khalipha yay yana wani nazari saboda maganar hajiya iya, yace, “Eh hakane Granny, amma dai yanzu akwai wasu hanyoyin da mace kan iya samun ciki koda babu alaƙar namiji a tsakaninsu”.
Cikin sauri hajiya iya tace, “Kai Khalipha kaji tsoron ALLAH ta wace hanyace kuwa? Ni dai ban taɓa jiba gaskiya”.
Murmushi Khalipha yayi, cike da rashin damuwa ko tunaninsa kaiwa nan ɗin da wata manufa yace, “Granny karki manta nifa Doctor ne. Doctor ɗinma dakeda alaƙa da matsaloli irin na mata. Akwai hanyoyi da dama kamar su yin dashen ciki da makamantansu”.
“Kamarya dashen ciki?”.
Dariya yayi yana miƙewa. “Oh oh Granny wannan ai bayanine mai zaman kansa. Amma dai ki sani yanzu ana iya dasama mace ciki ta haihu wlhy”.
Baki hajiya iya ta taɓe da faɗin, “Ah kudai da shegen ƙaƙale-ƙaƙalenku na likitoci dalilin yin karatu cikin masu jajayen kunnuwa ba. Mudai ko anayin wannan sheɗancin baije manaba kaji, danni wannan ai badan karna yanke hukunciba sai nace kamar wuce wuri ne”.
“Tab Granny wlhy mutanenmu ma sunayi, duk da dai gaskiya turawa sukafiyi, amma yanzu kinga kamar a kudancin ƙasarmu sosai sukeyi, wasuma sana'a suka maidashi wlhy. A dasa musu cikin idan lokacin haihuwarsa yayi su haifa suba masu cikin ɗansu. ALLAH dai ya ƙyauta, dan wasu tsiraru a mutanenmu ma sun tsunduma wannan harkar sosai musamman ƴan gayun mata da basa son wahala, sai su bada a ɗaukar musu cikin idan ya isa haihuwa a haifa a basu abinsu. Wasuma a asibitin ake ajiye musu ba jikin kowaba. Idan ya isa haihuwa a ciresa a basu”.
“Kai wannan masifa dami tai kama. A lallai wannan duniya tazo ƙarahe kuwa”.
“Sosai ma” Khalipha ya faɗa yana ƙoƙarin ficewa dan bayaso halin da yake ciki yakai ga bayyana a fuskarsa har Hajiya iya ta fahimta.
A falo ya wuce su Zinneerah dake kallo, yanda ya wuce ko kallonsu baiyiba yasa Jamal cewa, “Tofa, inaga Granny da Yah Khalipha anɗan dambacebe naga kamar ya wuce a fusace”.
Dariya su Meenal sukayi. Zinneerah ko tayi kamar bata jiba dan tun ɗazun gabanta ke wani irin faduwa. zuciyarya na mata rauni kamar maijin tsoron faruwar wani abu a gareta. Sai dai ta daure bata sanarma kowaba tanata addu'a a zuciyarta. Dan kallonma yinsa kawai take ba fahimta takeba sam.
Duk wannn abu dake faruwa Farah na ɗakinta cike da damuwa. Dan tunda taji AK ya tafi Nigeria zuciyarya bata samu nutsuwaba. Wannan dalilin ya sata kiran Aunty Zakiyya ta sanar mata, ta kuma turama Mammah text message. Aunty Zakiyya ce ta kira Mammah suka tattauna, duk da ba'a kano takeba Mammah ta bata damar sakawa a mata binciken zancen yaron.
Daga haka ta kira baffa a gadarance tana tabbatar masa bai isa rabata da AK ba. Idan ma wani abu yake ƙullawa sunyi ta banza, dan ko aure suka saka AK yayi har aka samu wannan yaron ya tabbatar sai AK ya saki koma ƴar uban wacece. taji zafin maganganun da Baffah ya yaɓa mata, dan haka ta yanke shawarar Aunty Zakiyya na gama mata bincike zata tafi Nigeria ɗin da kanta, shiyyasa ta kira Farah ta kwantar mata da hankali da mata nasiha akan karta sake shiga harkar kowa a gidan harsu gama bincikensu.
To wannan nasiha ta Mammah tasa Aunty Farah nutsuwa waje guda ita a dole ta kama kanta.😹. Suma dai su Hajiya iya daba sanin miya faru sukaiba babu wanda ya shiga harkar tata. Dan yanda bata nema ganin kowaba tun bayan tafiyar mijinta, suma sai basu nemetaba. Dan a matsayinta na matar gida ita keda haƙƙin bin yanda suka tashi ko sukaci suka sha a gidan. Amma bata taba yiba tayaya suma zasu takura kansu ne akan damuwa da al'amarinta. Gara su rike mutuncinsu ko za'a zauna lafiya.
Su Zinneerah kam koda suka fahimci ɗunbin farin cikin da hajiya iya ke a ciki suka tambayeta catai babu komai. dan sunyi magana da Baffah akan zasubar zancen kar Zinneerah ta sani har sai sun dawo Nigeria saboda sheɗancin su Mammah. Baffah yace yana tsoron su sani subi ta wata hanyar su cutar da yarinyar mutane a ƙasar da batasan kantaba. Amma tunda nan da sati biyu zasu koma ayi haƙurin hakan kawai dan za'a haɗe bikinne da nasu Ni'ima. Hajiya iya kuwa ta gamsu da wannan shwarar ɗari bisa ɗari. Dan haka bayan Khalipha tai gum da bakinta...........✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu😭🙏🏻_*
*_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
___________________
*Page 43*
...........A Nigeria kuwa yau cikin farin ciki AK yay barci rungume da Little, haka kawai wata nutsuwa da farin ciki suka mamayesa. Dukan wani ƙunci da damuwa da tunani akan samuwarsa suka kwaranye, farin ciki da nutsuwa suka maye gurbinsa, jiyake tamkar ya haɗiye abinsa ya ƙara haifosa tsabar yanda yakejin abun kamar almara. wai shine da ɗa da rana tsaka, ɗan da baisan ta yanda ya samar da shi ba, ɗan da baisan a ina ya samar dashi ba. Shi tsabar ma nazari akan waɗanan tambayoyi. har ji yake ƙwalwar kansa na kuɗa, shiyyasa ya tattare komai ya ajiye gefe ya rungumi ɗansa tare da sumbatar goshinsa yana murmushi.
Ya jima barci bai ɗaukesaba yanata kallon little ɗin, sai can kusan ɗaya na dare barci yay awan gaba da shi. ALLAH ya soshi yaron baida fitina. Dan bai farkaba sai gabannin asuba ya tashi yana kiran “Mama ruwa, mama ruwa”.
A hankali AK ya buɗe idanunsa, ya miƙa hannu ta bayansa ya kunna fitila dake a bedside drawer dan da alama basu da wuta. Zaune ya tashi da ƙyau yana riƙo little dake neman yin kuka yana kiran ruwa. “Oh oh sweetheart i'm sorry ina zuwa”. Ya faɗa da ɗagashi gaba ɗayansa ya maida jikinsa. Kafin ya ɗakko ruwan daya ajiye gefensu dan shima yakan tashi shan ruwan dare shiyyasa baya kwanciya babu shi a kusa. Sosai little yasha ruwan. Yana gamawa ya lafe a jikinsa ya koma barci. Shiru yay yana kallon fuskar yaron mai tsananin kama da tashi, wani lallausan murmushi da ajiyar zuciya suka kufce masa a lokaci ɗaya. Kwantar dashi yay a hankali yaja bargo ya rufa masa shi kuma ya sauka dan yasan bazai iya sake komawa barcinba kuma.
Harya fita sallar asuba ya dawo little nata barcinsa, shima sake kwanciyar yayi dan barcin yake buƙata.
Kusan takwas na safe ya farka dole saboda tsalle-tsallen da little ya farka yana masa a jiki, dole ya buɗe idanunsa da sukai nauyi irin na wanda ya tashi a barci. Kamo hanunsa yay ya zaunar a jikinsa yana murmushi tare da kai hannu ya shafi fuskarsa. “Little Handsome ka hanani barci bayan kai kasha naka”.
Cikin rashin damuwa little yace, “Abba tea”. Dariya AK ya ƙyarƙyale da shi yana miƙewa zaune dashi a jikinsa. “Wato kai yaren abinda kakeso kawai kake ganewa ko? Inga bakin shan tea ɗin?”.
Babu musu little ya ko wage masa baki alamar gashi. Dariya nanma ya sakeyi da sumbatar goshin yaron wani farin ciki na saukar masa. Huzaifa dake tsaye a ƙofar ɗaki yana kallonsu yay murmushi tare da jin daɗin ganin ɗan uwansa na walwala maiban mamaki, dan ba abu ƙarami bane a rayuwa ke saka AK ƙyalƙyala dariya. Baiyi magabana ya juya abinsa. Shiko AK daba ganinsa yayiba little ya ɗauka zuwa toilet, da kansa yay masa wanka, ya naɗo abinsa a towel ya kawo ɗaki ya ajiye a kan gado. Wayar Haneef ya kira yana tambayarsa sunzoma little ɗin da kaya ne?. Daga can Haneef ya amsa masa da eh bara ya kawo.
“Okay” ya amsa yana yanke wayar, game ya sakama little a waya ya nufi toilet ɗin shima yin wankan. Shigarsa babu jimawa sai ga Haneef, sai da yayi sallama sau kusan uku, jin ba'a amsaba ya leƙo da kansa. Little kawai ya hango yana kokawa da waya, dan haka ya shigo yana dariya. “My Darling good morning ” ya faɗa yana kaiwa tsugunne gaban gadon. Little dayay busy abinsa ya ɗan ɗago ya dubesa ya sake maida kansa.
Yanda yayi ɗin sai ya bama Haneef dariya, ya fisge wayar yana faɗin, “Haba my man ni zakama jama aji danka samu phone?”.
Ɓata fuska little yay zaiyi kuka Haneef ya maida masa wayar yana dariya. Daga haka ya miƙe ya ɗakko man Yayansu daya hanga a kan mirror yazo ya yayema little towel ɗin da yake a ciki ya hau shafa masa. Sunayi ana kokawa dan little baison ajiye wayar hannunsa. Har dai aka gama. Yana saka masa kaya AK ya fito. Gaidashi Haneef yayi. Ya amsa shikam yana binsu da kallo, dan yanda suke kokawa wajen saka kayan kawai zai tabbatar maka akwai shaƙuwa a tsakaninsu sosai.
Haneef na gama shirya little ya ɗaukesa suka fice danya bama Yayansu damar shiryawa. A hankali AK ya sauke numfashi, zama yay a bakin gadon yana ɗan kai hannu ya murza goshinsa, hakan yayi dai-dai da shigowar kira a wayarsa.
Kamar zai share sai kuma ya ɗauka wayar dake a kife, duk da ganin Mammah da yayi ɓaro-ɓaro a jikin screen ɗin bai kawo komai a ransa ba ya ɗaga.
Sama-sama ta amsa masa sallanarsa, gaisuwa kuwama bata amsaba ta shiga masa magana cikin faɗa. “Yanzu Abdul-Mutallab danka maidani banza harka iya ɗaukar ƙafa ka tafi Nigeria bakako sanar minba!!?”.
Idanunsa yaɗan lumshe da raunan muryarsa gareta kodan daraja ta uwa da ALLAH ya bata, cikin girgiza kai kamar yana a gabanta yace, “Am so sorry Mammah, nima tafiyar ta dolece wlhy, ki gafarceni”.
“Dole kace ta dolece tunda ubanka ya gama gayamin magana jiya, aiko yayi da ƴar halak da bazata raga masaba. Dan insha ALLAH yau zan baro london nima zuwa Nigeria ɗin, sai naga munafurcin da kuke son biznewa”.
Babu shiri AK ya miƙe yana faɗin “Mammah Nigeria kuma?”.
“Ƙwarai da gaske, ko karnazo ne ubana?!”.
Bakinsa ya cije dakai hannu ya dafe kansa, zaiyi magana ta yanke wayar ƙitt
Rasa abinyi AK yayi a ɗakin, ya shiga kai kawo kamar mai ɗawafi. Sam baiso Mammah tazo Nigeria a wannan gaɓar, dan yanda Baffah ya ɗauki zafi wlhy ba raga mata zaiyiba. Shiko baya buƙatar ganin suna shiga irin wannan rikicin dan ƙara nisantasu yakeyi.
Wayar Mahma ya kira da sauri dan yasan itace kawai zata iya takama Mammah birki. Harta tsinke ba'a ɗagaba, dan haka ya sake kira. Jin an ɗauka ya sauke ajiyar zuciya. Sai dai jin muryar Adilah na faɗin, “Sweet bro surprise”. Ya sakashi maida hannunsa a goshinsa yana murzawa. Ƙoƙarin dai-daita muryarsa yayi yace, “Uhmyim Darling badai kina london ba?”.
Ɓata fuska tayi daga can kamar tana gabansa. Cikin shagwaɓa tace, “Uhm ai dama nasan yanzu ka daina sona ALLAH, yau kwana biyu ina nemanka a waya saboda dawowana amma bana samunka, na dawo ɗazun nan, saina tarar wai kana 9ja, yanzu haka ina shirin tafiya can gidanka wajen Granny ne, ina jiran Khalipha yace zaizo mutafi idan ya fito school”.
“Oh parrot har yanzu dai baki canjaba. Ina Mahma ne?”.
Baki ta tura duk da kuwa bata kasance ƙaramar yarinyaba, dan tama girmi Khalipha da kusan shekara biyu. Cikin shagwaɓa tace, “Haka dai kakeson parrot ɗin nan taka. mahma gata can suna rikici da Mammah akan wai zatazo Nigeria ita da Farah. Wai mike faruwane na isketa sai faɗa faɗa, ni wlhy namaji dama ban dawo ba. Shiyyasa zan tafiyata gidanka dan banason faɗan nan na Mammah taita zagin mana Baffahn mu”.
Hankalin AK ne ya kuma tashi, atake raunin da yake ɓoyema ƴar uwarsa ya bayyana. Idanunsa suka sake kaɗawa sukai jajur. “Adilah akwai matsalane, amma yanzu sanin tushenta bashine abinyiba. Inason kije ki sace min passport ɗinta dana Farah ɗin duka”.
“Tab, wlhy Bro hakan dakamar wuya, dan inaga abinda Mahma tai niyyar yi kenan Mammah ɗin ta gani, yanzu hakama gata can harta fito da kayan tafiya shine Mammah ta kulle ƙofan ta canja security”.
“Thanks GOD”. Ya faɗa yana furzar da zazzafar iska. Hakan da yayine ya sake tayarda hankalin Adilah, dan ta tabbatar Yayanta na cikin damuwa, tambaya ta shiga masa amma bai iya bata amsa ko gudaba, sai ma yanke wayar yayi daga ƙarshe ya zame ya kwanta a gadon yana mai dafe kansa da yakejin ya fara sara masa da ƙarfi.
A cikin gida kuwa little nacan yanata hidimarsa a tsakanin su Baffah hankali kwance. Dan tare yay karin kumallo da Baffah da Mommy abinsa. Hakan harya dinga basu mamakin yanda ya saki jiki dasu sosai. Sai da suka kusa gamawa AK ya shigo falon. Gaidasu yayi sanan ya kai zaune kusa da Mommy. Ta shafa kansa cikin kulawa take faɗin, “Kana lafiya kuwa Son?”.
Ɗan ɗagowa yay daga kwanciyar da yay jikin kujerar yay mata murmushin yaƙe. “Lafiya lau Momy gajiyan jiyace kawai”.
“Aiko ya kamata ta sakeka haka. Kodai Daddy nane bai barka kayi barciba?”. Tai maganar tana kallon little dake wasansa hankali kwance. Shima kallon little ɗin yayi yaɗan ɗauke kansa da sakin guntun murmushi. “No Mommy, aishi wannan ko hidimarsa tasa idan ya kwanta bazai farkaba, kawai dai hajiyanne”.
“Ayya to sannu kaji, taso ka karya saika koma ka sake kwanciya ka huta”. Tai maganar tana faɗa haɗa masa abincin dake a tsakkiyar falon wanda basu jima da gama ciba suma. Baffah dai najinsu amma bai tankaba, sai dai yaji a ransa babu wata gajiya dake damun AK ɗin akwai dai dalili. Dan yanayinsa baiyi kama damai gajiyaba sai damuwa.
*_DANYA_*
Ba ƙaramin sake rikicewa Inna tai ba da ganin kayan goron ɗaurin aure wai duk na Zinneerah, yarinyar da aka cemata tana can ta kama ɗaki. Kai ina akwai ƙarya a wannan al'amarin. Kawai dai ta fahimci Baba da wani sabon salo ya dawo danya. Kawai yayi hakane dan ace ƴarsa na cikin aminci. To itako zata tabbatar masa ras take kallonsa.
Da wannan banzan tunanin nata yasa ta wartsake kamar babu abinda ya dameta. Sai ma ƙoƙari sakama kanta wata walwalar dole takeyi musamman idan ƴar barka da gulma suka shigo, dan zuwa yanzu duk zancen ɗaurin auren Zinneerah ya shiga garin na Danya. Wasu kuma badan barkar suke zuwabama yanzu dan son gani da idone da son tabbatarwa da abinda ke faruwa a gidan. Dawowar baba da sabuwar amarya harda tsohon ciki, auren Zinneerah da dawowar Karima gida.
Aiko dai suna ganin abinda sukazo neman, dan haka duk wacce zata fita saita gumtsi gulma ta fita dashi a baki, duk yanda Inna ke ƙoƙarin nuna ita ta dake ranta kishinta da damuwarta sun kasa ɓoyuwa, sai zabga habaici take wasu Baba da gugar zana. Har takai Gwaggo Laritu na maida mata a kaikaice itama.
Sai da baba yaga abin zai zama fitina ya lallaɓa Gwaggo Laritu ta wuce gida aka bar Inna da takaici dan kukan zuci kawai take faman yi wanda yafi na zahiri ciwo da cin rai.
___________________★
Koda AK ya kammala karyawa fita sukai shi da Huzaifa da little, dan yanason rage damuwar Mammah dake cin ransa suk da yaji daɗin abinda Mahma tayi. Sai da suka fita ya samu damar yin waya da Hajiya Iya ta wayar Khalipha daketa ƙoƙarin danne damuwarsa.
Sun jima suna wayar da Hajiya iya harma da Huzaifa da little dataji daɗin gani tare dasu dan video call ne. A bakin Hajiya iyan ne ma yakejin wai Farah ta fita da akwati a gidan tun ɗazun, kuma su basusan ina ta nufaba dan bataima kowa maganaba.
Murmushi AK yayi, cikin rashin damuwa yace, “Karki damu Granny gidan Mammah ta tafi, kuma Mahma zatai maganinta ne ta dawo da ƙafafunta”.
Baki Hajiya iya ta taɓe da faɗin, “Kai nifa yanzu kam taitayi dan bata cikin lissafina. Tunda ALLAH ya baka ƴar mutunci da nakeda tabbacin zata share hawayenka in ALLAH ya yarda. Fatana dai ka riƙemin yarinya da ƙyau Moddibo, dan wlhy inhar Inno tai kuka akanka kaima sai kayi”.
Fiska ya ɓata yana wani ɗan yatsinata. Yace, “Oh kukuma naku salon kenan Granny?”.
“Ai mun wucema haka, dan wlhy bazan baka Inno ba saina shimfiɗa maka dokoki, ko ɗaya ka tsallaka kuwa saika haɗu da fushina”.
“To lallai naku babbane, nikam sai anjimanki”.
“Zakaci ubanka Kabirune yaro, bauɗaɗen banza jikan ƴan Morocco”.
“Ahaka dai kuka gani kuka nane”. Ya faɗa a hasale saboda zagar masa uba da tayi. Itako Hajiya iya dama tayine danta hasalashi ɗin dan haka ta hau dariya. Huzaifa fa ma dai dariyar yakeyi. Hajiya iya tace, “Kaima ai ina zuwa kanka dan uwarka Balkisu, tuzurun banza kana neman tsofewa a gida babu aure. Why bara dai na dawo ƴar kowa na samu aura maka zanyi a dangi, da wani shegen kansa uwa sheƙar angulu”.
A take shima ya shanye tasa dariyar yana ɓata fuska, “To kin kuma dawo kaina? Kefa ALLAH Granny kinada matsa kiyita zagema mutum iyaye babu laifin zaune babu na tsaye. Sai ki nema wanda zaki samoma mata a ƙauye badai niba wlhy”.
“An zageka ɗin mai kama da zucbibin ƴan Lagos, bara dai na dawo kaga yanda zanyi maganinka wlhy, inba hakaba nasa Bashir ɗin yima uwarka kishiya itama wlhy. (Daddynsa take nufi😂) dan haka ya waro idanu waje da faɗin, “Kai! Wai ke Granny miyasa lamarin naki kullum gaba yakeyi?, sam bakison zaman lafiya?”.
“Oh bama kasan yana yin gaba ba saina dawo Nigeria”. Tai maganar tana yanke kiran.
“Tsohuwarnan akwai tarin matsaloli a kanta yasin”.
Cewar Huzaifa rai ɓace. Shi adole yaji haushi ance za'a saka aima Mommy kishiya😹.
“Ai indai Granny ce ta wuce duk yanda kake tunaninta”. Cewar AK yana wani ɓata fuska shima. Little da baisan anaiba wasansa kawai yake zabgawa.
Biyawa sukai ta gidan Dr Mahmud suka ɗaukesa dan gona zasuje duba masu aikin shinkafa, daga na su leƙa company da ayanzu haka an fara zuba aikinsa shima. Kasancewar sun tahoma Little da kayan ciye-ciye ko damuwa baiyiba, sai uban rashinji yake zubawa a gonar alamar yana cikin ƙoshin lafiya.
Huzaifa akwai son irin wannan wajajen, dan haka ya shiga cikin gonar sosai yana duba aikin da yaba ƙyawun da yayi. Da wannan damar AK da Dr Mahmud suka tattauna akan abinda ya shafesu game da ginin company nin shinkafa da kuma aikin shinkafar, dan a shirinsa so yake ya koma london zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu, kuma da Little yake shirin komawar, baisan kuma yanda zasu kwashe da Baffah ba akan hakan.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
[10/13, 2:25 PM] Mom Farooq: *_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
________________________
*page 44*
...........A gajiye suka shigo gidan gab da magriba, dama sun ajiye Dr Mahmud a gidansa. Little kuwa yayi barci jikin Abbansa dan Huzaifa ne yay driving ɗin.
Koda Huzaifa yay fakin a inda ya dace AK fita yay ɗauke da little a kafaɗa, kai tsaye sashen Hajiya iya ya nufa batare da ya saurari maganar da Huzaifa ke masaba. Kasancewar bayan tafiyarsu Abidah ta shigo ta gyara masa sashen sai ko ina ya kasance ƙal ga kuma ƙamshi, sosai yakejin kewar rashin Granny a sashen. Dan haka baima son zama ya yini a gidan sam.
A hankali ya kwantar da little dake barcinsa. Duk da ya ɓata jikinsa sosai a can bai tadashiba, sai dai shi ya cire nasa kayan ya nufi bayi a gurguje saboda lokacin sallar magrib yayi.
Wankan ma a gaggauce ya yisa ya fito, jallabiya kawai ya zura ya ɗan saka turare ya fito yana addu'ar ALLAH yasa kar little ya farka harya dawo.
Bayan an idar da salla bai zaunaba ya nufo gida saboda tunanin barin little da yayi shi kaɗai. Koda ya leƙo yaga barcinsa yake har yanzu sai ya koma massallacin. Sai da akai sallar isha'i suka taho shi da ƴan uwansa da Baffah gwanin sha'awa.
A gajiye yake matuƙa, dan haka ya wuce sashen hajiya iya kai tsaye yana cema Mas'ood yasa cikinsu Safiyya wani ya kawo masa tea da abinci kaɗan saboda little karya farka ya nema. Da to Mas'ood ya amsa masa cikin girmamawa.
Harya nufi hanyar sashen hajiya iya baffah dake ƙoƙarin shigewa nasa sashe shima ya juyi ya dubi AK ɗin. “Karfa suga mun musu ƙarfa-ƙarfa akan yaron nan, daga zuwa ya gaida Bilkisu”.
Juyiwa AK yay zuciyarsa na harbawa, harga ALLAH baya fatan abinda zaisa Baffah yace ya sake rabuwa da little ɗin a yanzu, danshi yanzu haka yana shiryama zuciyarsa tafiya da yaron nema london. Amma yanzu sai ya ɗan murmusa, murya a sanyaye yace, “Baffah zai koma ai sonake saina tashi tafiya”.
“Sai da safe”. Baffah ya faɗa yana shigewarsa. Shima cigaba yay da tafiya zuciyarsa na masa rauni akan iya sake rabuwa da gudan jinin nasa gaskiya.
Washe gari da safe bayan idar da sallar asuba koda suka dawo sake kwanciya yayi, dan cikin dare Little ya farka da kuka, sai da yay masa wanka ya bashi abinci suka sami salama. Shiyyasa yau ya tashi kansa na masa ciwo. To ɗan barcin daya samu ya sake komawane kuma yana tsaka ya ringajin hayaniya na tashi sama-sama a cikin sashen nasu. Duk yanda yaso daurewa karya tashi hakan ya gagara. Dole ya miƙe da ƙyar yana jan tsaki. Mamaki ya kamashi ganin babu little a ɗakin, tashi yay ya zira doguwar riga bayan ya shiga toilet ya fito, yasa Slippers ya fita. Ganin babu little a ɗan corridor ɗin wajen nanma ya fita da sauri, abinda ya gani ya sakashi tsayawa cak. Ashe a falon hajiya iya ake hayaniyar shiyyasa yake jinta sosai. Ba kuma kowa keyiba sai Mammahn sa, Farah na gefenta tana kuka kamar zata shiɗe.
Yabi Baffah dake ɗauke da little da kallo, daga shi har Mommy suna zaune kawai sun zubama Mammah idanu tana ta zabga musu azabar masifa akan abinda shi yama kasa fahimta kai tsaye. A matan gidan Momie ce kawai, dan ita kaɗai Baffah ya bama damar zuwa lokacin da Saifudden yazo ya sanar masa da zuwan Farah da Mammah duk da sau ɗaya ya taɓa ganinta kuma suna yara sannan, amma tsananin kamarta da Yayansu yasa yaji a ransa lallai itace Mammah, hakama yaran babu ko ɗaya a waje sai Huzaifa kawai.
Ji AK yayi tamkar ya fasa kuka dan takaici, dan har cikin ransa yaji haushin wannan zuwa da sukai. A hankali ya fara takowa zuwa tsakkiyar falon cikin izzar da fushi ya haddasa masa, fuskarnan tai kicin-kicin kamar zata fashe dan ɓacin rai.
Wani shegen tsawa data saka little fashewa da kuka yana ƙanƙame Baffah ya dakama Farah dake ƙoƙarin fara magana dan daga ita har Mammah basuga zuwansa wajenba. Ba Farah ba har Mammah sai da tai ɓam da bakinta ta juyo tana tana kallonsa ranta a matuƙar ɓace.
Yi yay kamar baiga Mammah ba ya fara saukema Farah duk fushin nasa. “Da izinin ubanwa kikazo Nigeria? Wai Farah kin maidani ɗan iskane da duk abinda ranki ya raya miki kikeyinsa komi?. Ki maida hankalinki fa.......”
A fusace Mammah ta katsesa da cewar, “Ubanka yace tazo, taƙi ta maida hankalin nata kuma, yanzu nan Abdul-Mutallab ko kunyar ALLAH bakaji a gabana kake cimata mutunci?”.
“Mammah!” ya faɗa ransa a ɓace, danya fahimci idan har ba nuna mata ɓacin ran nasa yayiba itama to zata cigaba da bauɗar masa da Farah da banzar aƙidarta. Cikin rufewar ido yace, “Please Mammah ba maganar wasa nakeba, wane kalar rashin mutuncine sai dai ta ɗauka ƙafa daga wata ƙasa ta taho bada izinina ba, kodan taga wancan karon na mata shirune? To wlhy ni bazan ɗauka wannan iskancin ba, na bata nanda awanni goma ta koma inda ta fito, inba hakaba wlhy saina tabbatar mata da ainahina na Abdul-Mutallab Kabeer Abdul-Mutallab Shira”.
Daga haka ya juya ya koma ɗakinsa. Wani ɗan murmushi Baffah yayi na manya ganin yanda Mammah tabi AK da kallo baki buɗe kamar sokuwa. Ƙara rungumesa little yayi da sumbatar goshinsa, shiko yaro ya ƙara lafe masa a jiki saboda tsorata da bala'in daddynsa.
Juyowa Mammah tayi tana kallon Baffah cike da tashin hankali. Idanu ya ɗan waro mata alamar minene? murmushi ɗauke a fuskarsa har yanzu.
Ƙara ƙufula tai da salon nasa, dan babu abinda ta gani sai Kabeer ɗinta masoyinta na da, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Kabeer haka ka maidamin yaro?”.
“Dama haka kika haifi abinki”. Baffah ya bata amsa kansa tsaye yana sake sumbatar goshin little. Sai kuma ya kalleta yana ƴar dariya, “Hindatu ko iya haka muka tsaya kin sami amsarki akan Adnan, dan kinji dai abinda yace, sunansa Abdul-Mutallab Kabeer Abdul-Mutallab Shira. Ba Abdul-Mutallab Hindatu Umar Kaita ba. Ballantana yanzu muka fara wasan ni da ke wlhy, dan sai na tabbatar miki ke kaɗai kikazo gidan nan badasu ba”.
“Kabeer Shira!”.
Ta faɗa a tsawace.
Shima Baffah a fusacen yace,
“Yes! I am. Hindatu Kaita!”.
Ganin yanda Baffah da Mammah sukai ɗin ya tayarma Mommy da Momie hankali, shi kansa Huzaifa ƙarjinsa sai bugawa yake dan tamkar AK yake bayason hayaniya, barshi dai da shegen surutu shima yafiyi ga wanda ya sani sosai. Farah kuwa ai sake tsurewa tayi dan bata taɓa tunanin haka Baffah yakeba. Kallon mutum mai sauƙin kan tsiya take masa.
“Dan ALLAH kuyi haƙuri ni banga abin tashin hankali ananba Yaya”. Mommy ta faɗa hankalinta tashe tana dawowa kusa da Baffah.
A fusace Mammah ta miƙe tare da kama hannun Farah da duk jikinta ke ɓari. Ta duba Baffah da manyan idanunta da har ƙwalla suke tarawa dan bala'i. “Banzo Nigeria da niyar yin fitina da kai ba Kabeer, amma tunda har kace ka shirya muje zuwa. Ina mai tabbatar maka bazan bar ƙasar nanba sai da yarona, sai kuma nasan uwar data haifa wannan ɗan da shi. In ko har aure ka ɗaura masa da ita aka samar da shi sai ya saketa, na haɗa da yaron kuma na wuce, dan yazama nawa shima”.
Wata ƴar dariya ce ta suɓucema Baffah babu zato, ya shafa kan Little yanayin kayarsa hankali kwance. Kafin ya ɗago yana nuna mata little. “Wannan shine tunani mafi gurɓata da kika taɓayi a rayuwarki Hindatu, kinsanfa ance abin cikin ƙwan yafi ƙwan daɗi. Dan haka ki sani wannan da kike gani zuciyata ne da duk ma wanda yake rayuwa a gidan nan. Kinsan kuwa raba zuciya da gangar jiki abune mai wahala ga ɓarawo. Amma tunda kema kin shirya wasan muzuba, ɗan halak ka fasa. Sai dai ki sani wasa zamuyi da basira bada hauka ba. Ki cire wannan shirmen a ranki ki nutsu waje guda wajen farautar dawo da Abdul-Mutallab gareki, nima zanyi farautar ganin ya dawo gareni daga shi har Maryam (Adilah) sannan kuma na haɗa da ɗan jikallena abin cikin ƙwan”. Ya ƙare da wani salon ɗage mata gira ɗaya.
Da ƙarfi ta rumtse ido da cije baki, harshenta har harɗewa yake wajen ambaton, “Muje zuwa mana, kaima kasan Hindatu, nama ƙwata ada da kake jin kanka Kabeer Shira balle yanzun. Wlhy saina tabbatar maka dani Hindatu bakatsiniyace ƴar asali”.
“Kika dai sata. Kamar yanda nima sai na ƙara tabbatar miki dani Kabeer jinin bauchi ne gaba da baya babu gauraye”.
Fuuuuu Mammah taja hannun Farah dake kuka dan duk a firgice take suka fice. Dama tun jiya da dare suka iso a hotel sukai masauki.
“Amma Yaya miyasa zaka biye mata? Kasan fa Hindatu dama can ƴar zafin kai ce. Dan ALLAH karku saka yaranku a rikicinku, gashi ma harda jiƙa da shi baima gama saninkuba da ƙyau har yanzun”.
Murmushi Baffah yayi yana kallon little. Hankalinsa kwance yace, “Zai sammu ne Bilkisu. Zafin kan Hindatu kuwa zan sauke mata shi a wannan karon dan na fita itama ta sani. Wasu dalilaine kawai yasa na barta ko a can baya ɗinma”.
Shiru falon yayi zuciyar kowa da fargaba. Musamman ma Momie da ayanzu ta gama sallama ma bala'i da gadarar Hindatu.
Silalewa Huzaifa yayi ya fice, dan abinda kawai zuciyarsa ke basa da wannan game ɗin kafin a farashi Hajiya iya ta dawo gidan nan. Inba hakaba Mammah zata iya bin ta wata hanyar ta sace koda little ne ta gudu dashi idan Ak ya gagareta a yanzun. Wayar Khalipha ya kira.
A lokacin yana kwance zazzaɓi ya rufesa, dan duk yanda yaketa ƙoƙarin danne damuwar rasa Zinneerah hakan na neman fallasa kansa. Amma dai yanata roƙon ALLAH ya rufa masa asiri ya cire masa ita a rai, dan baya buƙatar Yayansu dawowa ya gansa a wannan halin. Ɗagawa yay cikin dauriya, bayan sun gaisa Huzaifa ke tambayarsa ko lafiya?. Cikin dakewa yace masa a barci ya tashi.
Cikin gamsuwa Huzaifa yace ya haɗasa da Hajiya iya, shima kuma ya zauna a wajenta dan maganar ta shafesa. Amsa masa da to Khalipha yayi yana tashi ya fito. A falo ya samesu su duka zaune suna hira da kallo. Ya miƙama Hajiya iya wayar yana sanar mata Huzaifa ne.
Amsa tai cikin tsokana ta fara da faɗin, “Ɗan nema mun shirya kenan? Bandama abinka nima ai bazanso aima autata kishiya ba”.
Damuwar da Huzaifa ke a ciki ta tashin hankalin daya gani ya sakashi cewa “Granny magana zamuyi ni dake da Khalipha ”.
“Lafiya dai ko?”.
“Da sauƙi dai”.
Tsaye hajiya iya ta miƙe tabar wajen zuwa ɗaki Khalipha ya bita. Daga haka Huzaifa ya yanke kiran shi kuma ya kirasu a video call. Bai ɓoyema Hajiya iya da Khalipha komaiba daya gama faruwa yanzun nan. Cikin matsanancin mamaki Khalipha yace, “Dama Nigeria wai su aunty Farah ɗin suka taho?”..
“Gasu harma suna ƙulla game da Baffah. Granny inaga ki dawo gaskiya dan wannan al'amarin ba wasa bane. Na tabbata Mammah zata iya sace little shima, dan nidai yanda ta nuna ɗin na tsorata. Ni kuma wlhy yanda na fahimci Yayanmu nason Abdul-Mutallab banason ta rabashi da shi. Bama shiba koni yaron ya shiga raina. Hakama yaran gidan nan wlhy suna tsananin ƙaunarsa, dan yanda suka shaƙu da shi aduk da ba gidan yake ba ya isa amsa gamai kallo. Khalipha zan turo kuɗi a shiyama Granny tahowa, idan lokacin ganin likitan yayi saita koma”.
Cikin gamsuwa Khalipha ya gyaɗa masa kai kawai. Dan shima ya gamsu da hakan, shi kansa zai bisu dan yasan Yayansu nacan cikin damuwa da tashin hankaki dama gashi ya tafi a birkice.
A ɓangaren AK kam koda ya koma ɗakinsa duk abinda ke faruwa tsakanin Baffah da Mammah yana jiyosa, har game ɗin da suka ƙulla tsaf yaji, mamakin Mammah ya sake kamashi jin kuma little ɗinma ya zama abin harinta bayan ita ta gama bala'i ranar a london.
Safa da marwa ya shigayi a ɗakin yana tunani da nazarin matakin dazai ɗauka akan Farah dan harga ALLAH yana tsoron Mammah ta cigaba da busar masa da idonta akan wannan halayen da sam basa birgesa. Dolene yayi wani abu kafin wankin hula ya kaisa dare.
Ciwon da kansa ke masane ya sakashi tattara komai ya ajiye ya koma gado ya kwanta. Duk da tarin ayyukan dake garesa a yinin yau dan yanason komawa london gobe idan ALLAH ya kaimu baijin zai iya fita a gidan. Maganar komawama babu ita tunda su Mammah sukazo nan ɗin. Dan dole ya haƙura har sai yaga sun koma.
_________________★
Babu wanda yasan mi Huzaifa ya ƙulla. Cikin dare sai ga baƙin london. AK na zaune bisa sallaya yana karatun Al-qur'ani bayan kammala nafilfilinsa ya ɗanji maganganu sama-sama. Mamaki ya kamashi duk tunaninsa Farah da Mammah ne suka kwana a gidan, dan shi da wuri yay barci jiya saboda allura da Dr Mahmud yazo yay masa kasancewar jininsa ya hau sama sosai dalilin ɓacin ran safiyar jiyan. Little ma yau a wajen su Momie ya kwana, tunma fitar da Baffah yay dashi bai sake ganisa ba sai da yamma Huzaifa ya shigo tare dashi duba jikinsa. Da Abidah kuma ta shigo kawo musu abinci ya maƙale mata.
Bai tashi ba sai da yakai inda ya dace, Al-qur'anin ya rufe ya tashi ya fita a ɗakin. Turus ya tsaya yana kallonsu Meenal dake shigowa da kaya, ga Hajiya iya zaune cikin kujera tana shan ruwan da Zinneerah ta ɗakko mata a kitchen. Murmushin kwantar da hankali Hajiya Iya tai masa. Yayinda su Jamal suka shiga gaishesa murya ƙasa-ƙasa dan darene sosai kusan ƙarfe uku ma.
Da ƙyar ya iya ɗaga ƙafarsa ya tako garesu, Zinneerah da sai yanzu hankalintama yakai garesa dan ta juya baya a yanda take tsaye ta ɗan matsa ta bashi hanya murya ƙasa-ƙasa tace, “Barka da dare Yayanmu”............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
[10/13, 2:25 PM] Mom Farooq: *_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_________________________
*Page 45*
...........Sai da ya kai zaune sannan ya ɗan dubeta ya kauda kansa yana maidawa ga Hajiya iya mamaki har yanzu shimfiɗe a fuskarsa. Kansa ta shafa tana murmushi. “Mamaki ko?”. Ta faɗa tana kamo hannunsa cikin nata.
Cikin ɗacin murya yace, “Amma Granny yanz......”
“Shiii” ta faɗa tana girgiza masa kanta alamar kar yace komai. Badan yasoba dole yay shiru yana binta da kallo. Barin wajen Zinneerah tayi dan kasancewarsa a wajen yasa taji ya cika mata fili kamar yanda takeji a duk sanda yana a waje. Handbag ɗin Hajiya iya ta ɗauka tabi bayan su Bahijja da har sun shige, barci da gajiyar da take ciki ya haddasama tafiyar tata sanyi sosai fiye da ko yaushe.
Shigowar Khalipha ya sanya Ak dake binta da kallo juyawa ya dubesa. Murmushin ƙarfin hali Khalipha yayi da matsowa ya rungumesa yana jera masa kalmar “I'm sorry yayanmu”.
Komai baice masaba, sai kansa kawai daya ɗan kaɗa yana miƙewa. “Dare yariga yayi nisa, yakamata ku kwanta ku rage gajiya”. Daga haka ya nufi ɗakinsa ransa duk babu daɗi da dawowar tasu, dan shi ba haka yaso ba.
Ƴan gidan babu wanda yasan da dawowar ƴan london sai washe gari, a take suka rikice da murnar dawowar Granny, yayinda Baffah kuma keta mamaki, sai dai dariyar da yaga Huzaifa nayi suna magana da Khalipha ƙasa-ƙasa ya sashi fahimtar sune suka ƙulla komai. Uffan baiceba ya shiga layin ƴan murnar ganin hajiya iya shima.
Sai da duk suka lafa da gaishe-gaishe da tambayar jiki sannan su Zinneerah suka fito suka gaida Baffah suma. Cike da jin daɗi da kulawa yake amsa, dan ƴan kwanakin da sukai acan harsun ƙara canja kala.
Sai da kowa ya nutsa sannan Baffah ya samu zama da Granny shi da Mommy da hajiya iya keta murnar ganinta da kiranta autarta. Yanda Mommy ke nane da hajiya iya sai hakan ya birge Zinneerah har little ɗinta ya faɗo mata a rai da mamanta itama da baba. Murmushi tayi a zuciyarta tana mai begen ganinsu.
Kamo hannunta Mommy tayi ta zaunar kusa da ita tana faɗin, “Masha ALLAHU, lallai yarona ya iya zaɓe, dan ɗiyar tawa kam badaga nanba”.
Kunyace ta kama Zinneerah duk da bata fahimci inda zancen na Mommy ya dosaba. Sai kuma can gefen zuciyarta ke raya mata ko dai Moos'ab ya faɗa musu wani abune?. Sosai gabanta ya faɗi, taɗan saci kallon Khalipha dake ƙoƙarin fita zuciyarta na bugawa da sauri-sauri. Bata gama kammala tunanintaba ta miƙe ganin kowa ya fice a yaran sai ita kaɗai. Itama ficewa tai tabar su Granny dan taga alamar magana zasuyi.
Kayan barcine wando da riga a jikinta, sai dai ta ɗora hijjab mai hannu a sama kalar pink mai haske daya kai mata har gwiwa, gashi ya ɗau guga dan da zatai salla ta cirosa ta saka.
Fitowarta dai-dai da shigowar AK ɗauke da little a hannu, kamar daga sama taji muryar gudan jininta na ambaton, “Aunty! Aunty!”.
Da sauri ta ɗago ta kalli hanyar shigowar duk da zuciyarta bata yarda da abinda tajin ba. Cikin sa'a kuwa sai a kan little daketa zillo daga jikin AK alamar zaizo wajenta. Shiko yaƙi sakinsa sai ma kafeta yay da idanu kai tsaye hankalinsa kwance.
A hankali ta motsa laɓɓanta wajen ambaton “Little” da mamaki shimfiɗe a saman fuskarta. Ga wani bugawa da ƙirjinta keyi saboda matsanancin kamannin yaron nata da Yayansu da suke ƙara bayyana kansu a koda yaushe. Musamman yau da fuskarsu ke gab da juna kuma little ɗin tamkar ya ƙara girma da wayo.
Duk yanda taso ɗaga ƙafarta zuwa garesu ta amshi little ɗin ta kasa, haka ta cigaba da tsayuwa harshi ya fara takowa a hankali yana nufota. Tsitt falon yayi kowa ya zuba musu idanu ƙasa-ƙasa, musamman su Mas'ood da sukasan mike tsakani yanzun. Su Jamal dai yanda Yayan nasu ke kallon Zinneerah ɗinne da yanda tayi itama ya basu kala suka tsaya kallo dan son ganin mike shirin faruwa.
Gab da ita ya tsaya, batare da yayi maganaba ya kamo hannunta ɗaya ya ɗaura na little akai. Kafin ya saki yaron gaba ɗaya gareta yana motsa laɓɓansa a hankali yanda ita kaɗai zata iya jinsa, itama ɗin sai da taimakon motsin laɓɓansa. “Sai na tsone wannan idanun”.
Sosai taji wani irin shock saboda jin hannayensa da nata na neman sarƙewa waje guda lokacin da yake sake mata little, magarsa da yanayin da ta ji ya sata tura baki da ɗan juya kwayoyin idon dazai tsokale batare da tasan tayiba.
Leɓensa na ƙasa ya wani cije ganin yanda ta tura baki ga idanunta sun fara tara ƙwalla suna wani farfar. Ya saki wani munafikin murmushi da ya nema sakata sakin little ɗin ƙasa yana ja da baya. Da wani irin slow tafiya ya raɓata ya wuce ƙamshin turarensa na sake bugun hancinta.
Babu shiri ta ƙanƙame little jin zai suɓuce mata. Suko su Saifudden suka shiga sunne kawuna ƙasa suna dariyar shaƙiyanci ƙasa-ƙasa. Su Bahijja kuma da basusan dawan garinba bakuna suka saki cike da mamaki da al'ajabin abinda Yayan nasu yayi yanzun, amma ya fiske ya wucesu tamkar baisan da zamansu a wajen ba.
Yana shigewa ɗakin Hajiya iya su Mas'ood suka shiga tafawa da juna. Khalipha yay ƙasa da kansa yana sakin murmushi da ƙoƙarin kauda komai dake ransa dan yasan dai ta ƙare. Koda ace ya furtama Zinneerah so Yayansu ya nuna yanaso wlhy zai iya sadaukar masa. Ballema ALLAH ya soshi bai taɓa koda nuna mataba duk da kuwa tun sanda ya haɗu da ita a gidan tai caraf da zuciyarsa. Dan bazai saka haɗuwarsu ta farko a lissafi ba, saboda kallon matar aure yake mata. Duk abinda yay mata kuma tausayine a wancan lokacin ba so ba.
Moos'ab ma dai daurewa yake matuƙa wajen danne komai, dan yayi alƙawarin koda yaƙi sai ya cire Zinneerah a ransa ta koma matsayin matar Yaya da ƙanwarsa har cikin zuciya.
Zinneerah kam ƙanƙame little tayi a jikinta da sauri mamakin abinda Yayansu yayi na neman kasheta da ranta. Ta bisa da kallo harya shige ɗakin hajiya iya ko waiwayosu baiyiba. “Aunty!!” little ya faɗa da ƙarfi cikin kunnenta yana bubbuga mata kafaɗa. Babu shiri ta juyo garesa tana sauke tagwayen ajiyar zuciya. Sai kuma ta saki murmushi da lakace hancin little ɗin tana faɗin, “Haba bawan ALLAH kashemin dodon kune zakayi ne? Waya kawoka nan?”.
Bata da mai bata amsa. Danshi little ma dariyarsa ya saki maiban sha'awa saboda lakace masa hanci da tayi, ya kwanta a kafaɗarta yana zagayo hannunsa ɗaya a wuyanta zuwa ɗayar kafaɗarta. Hannunta ta ɗora akan gadon bayansa tana shafawa a hankali da murmushi, murya ƙasa-ƙasa tace, “I miss you my heart, ALLAH ya albarkaci rayuwarka, ya baka kariya a kowanne sakan na agogo”.
A ɗakin hajiya iya kuwa koda AK ya shiga tararwa yay su Baffah na magana. Baffah na zayyanema Hajiya iyan yanda sukai da Mammah. Gaishesu yayi, duk suka amsa masa da kulawa. ya yunƙura da nufin fitowa ya basu waje Hajiya iya ta dakatar dashi ranta a ɓace dajin abinda Mammah tazo tayi.
Komawa yayi ya zauna kansa a ƙasa dan yaƙi yarda ya kalli kowansu, bayason suga damuwar dake kwance a cikin idanunsa.
Cikin kaushin murya Hajiya iya tace, “Ina maka murna da samun yarinyar ƙwarai kamar Zinneerah moddibo, itama kuma ina tayata murna da samunka matsayin miji. duk da har yanzu zuciyata ta gaza hasaso ko tunanin ta yanda kuka samar da Abdul-Mutallab. Amma a dalilin wani bayani da Khalipha yaymin yasani shiga wasuwasi, zuciyata kuma ta ƙara shiga ruɗani da bayanin mahaifinka akan abinda ya faru randa aka sanar maka yaron jininka ne. Sai dai hakan dakai ba shike nuna zan yarda dakai ɗari bisa ɗari ba Moddibo har saina san gaskiyar al'amarin nan. Amma zan cigaba da roƙon ALLAH ya bayyanamin gaskiyar kafin nabar duniya. Ada nayi tunanin barin tarewar Zinneerah harta kammala karatunta na sakandire. Yanzu kuma na canja shawara saboda dalilai masu yawa. Ciki kuwa harda gadaran da mahaifiyarka keson nuna mana akanka da ƴar uwarka, tunda dai ita na fahimci batasan kawaiciba. Kaje daga yau ka fara gyaran gidanka, ka kuma shirya haɗama Inno lefe dan nan da kwanaki goma zata tare”.
Ba AK kawai ba hatta Baffah da Mommy sai da suka ɗago suka kalli Hajiya iya. Cinkin ɗan rawar baki Baffah yace, “Amma Inna karatunta fa?”.
“Tayi a gidansa”.
Ta bama Baffah amsa kai tsaye babu alamar wasa ko sassauci a saman fuskarta. Ɗan ajiyar zuciya Baffah ya sauke duk da shima bawai yana nufin wani dogon zango Zinneerah zata kaiba. Dama dai tunaninsa bai wuce ta gama zana jarabawarta ta ssce da zasu fara kwanan nanba. Amma kuma tunda hajiya iya ta yanke hukunci shi hakan ya masa kodan ya sake tabbatarma Hindatu shine boss.
Mommy ce tai ɗan murmushi tana kallon hajiya iyan, cikin kwantar da murya tace, “Innarmu baƙya ganin anyi gaggawa. Mu bashi damar shiryawa a tsanake sai a haɗa danasu Ni'ima tunda wata biyu ne kawai ya rage”.
“Na riga na gama yanke hukunci Bilkisu, ba kuma zan canjaba saboda shine dai-dai. Anjima kaɗan za'a kaini gidan Hauwa'u itama”.
Dole Baffah da Mommy suka amsa da to, AK kuwa uffan baice mataba. Dan shi yanzuma hankalinsa ba'a kansu yakeba. Tunanin wace magana? Khalipha ya sanarma Hajiya iyan yakeyi.
Ganin yanda yayi ɗinne yasa hajiya iya kallonsa a ƙufule. “Saboda an manna maka abinda ka ɓata yasa kaimin shiru Abdul-Mutallab?”.
Yanda ta faɗi real name nashi ya tabbatar masa da har zuciyarta ne. Dan haka ya ɗago ya kalleta, wani ɗan murmushi ya sakar mata yana miƙewa, “Indai nine kamar ki ɓata ranki, duk yanda kikeso haka za'ayi”.
Daga haka ya nufi ƙofar fita abinsa.
Su duka da kallo suka bisa. Hajiya iya dake masa kallon harara tace, “Munafuki kama fito ka faɗa kowa ya sani”.
Babu shiri dariya ta suɓucema Baffah da Mommy, dan yanda Granny tai maganar dolene ta baka dariya. Itako tai kicin-kicin da fuska kamar ba ita ta faɗa ba.
Koda AK ya fita baiko kalli kowa a falonba ya fice, garden ya nufa kai tsaye, yana shiga ya ciro wayarsa a aljihu ya dannama Khalipha kira. Cikin sa'a kuwa ta shiga. Ring ɗaya ana biyu Khalipha ya ɗaga dan yaga sanda Yayan nasu ya fita daga falon kamar a fusace.
“Ka sameni a garden”. Ya faɗa kawai yana yankewa.
Miƙewa Khalipha yayi da sauri ya fice shima sauran yaran na binsa da kallo. Tun kafin ya ƙaraso cikin garden ɗin ya hango AK daketa safa da narwa hannayensa duka biyu goye a bayansa. Sai da ya iso daf da shi sannan yay sallama. Juyowa AK yayi ya zuba masa birkitattun idanunsa da suka gama tsorata Khaliphan a take. Duk yanda yaso daurewa sai ya kasa dole ya risinar da kansa ƙasa. Cikin harɗewar harshe yace, “Yayanmu gani”.
“Na ganka ai”.
AK ya faɗa yana nufar kujera ya zauna. Fahimtar da Khalipha yayi yau a yaya yake ba besty ba sai ya nufesa shima ya zauna kusa da shi cikin rauni.
“Yayanmu wani abu ya faru ne?”.
“Zai dai faru Khalipha”.
Ƙara daurewa Khalipha yayi, dan shi duk tunaninsa ko Yayansu bayason auren Zinneerah ne, duk da yanajin zafin rasata bazai so Yayansu rabuwa da itaba dan sun dace. Duk da kuma yanada mata ya fisu buƙatar Zinneerah a yanzu.
Cikin nuna damuwarsa a bayyane yace, “Yayanmu dan ALLAH miya faru? Wlhy tsoratani kake sakeyi”.
Kamar AK bazai tankaba sai kuma ya gyara zamansa yana duban Khalipha ɗin da ƙyau. Zazzafar iska ya furzar idanunsa na sake rinewa. Kai tsaye yace, “Wace magana kukai da Granny?”.
“Granny kuma? Ni?”.
Khalipha ya faɗa cikin jinjinawa da son tunanowa.
Shiru AK yayi baice komaiba. Hakan ya bama Khalipha damar shiga kundin tunani na tsahon mintuna huɗu. Sai kuma ya duba AK yana ɗan jinjina kansa. “A sanina dai gaskiya babu wata magana da nayi da ita. In badai akan maganar IV......”.
Sai kuma ya kasa ƙarasawa.
Da idanu AK yay masa alamar cigaba. Dole Khalipha ya ɗan haɗiye yawu yana maida kansa kasa. Maganar da suka tattauna da Hajiya iya akan hanyoyin iya samuwar ciki ya sanar masa. Har yakai aya AK baice komaiba, dan tun a fara bayanin ya raba hankalinsa biyu, ɗaya ga Khalipha ɗaya ga nazari da fashin baƙin dukkan kalma ɗaya dake fita a zancen Khalipha ɗin.
“Amma kai miyasa kayi wannan hasashen?”. AK yay tambayar yana duban Khalipha cikin ido.
“Ba hasashe nayiba Yayanmu, kawai dai yanda ita Granny tai maganar hanyoyin iya samuwar cikine sai ta dalili ɗaya yasa nai mata fashin baƙi akai cewar yanzu akwai wasu hanyoyi da suka ɓullo a likitance. Ni wlhy bamma ɗauka zata riƙi maganar serious ba sam”.
Karan farko AK ya saki wani lallausan murmushi da ɗaura hannunsa akan kafaɗar Khalipha ya dan bubbuga tare da miƙewa. Daga haka baice komaiba ya nufi barin garden ɗin yabar Khalipha binsa da kallo.
Sai da ya ɓacema ganinsa sannan ya sauke numfashi shima da ɗaura hannunsa akan kumatu yayi tagumi. A fili ya furta, ‘Anya kuwa nima ban cancanci yin nazari akan wannan batunba. Gashi dai na faɗama Granny ne kawai bada wani daliliba. Amma yanda Yayanmu yay serious a maganar da yanda ya dage akan shi bai aikata komai akan samuwar Abdul-Mutallab ba kamar akwai ruɗani’.
‘Tabbas akwai ruɗani’. Khalipha ya sake faɗa yana miƙewa zaram tamkar wanda aka tsikara. Domin shikam dai akwai abinda dama ya tsaya masa a rai game da cikin da akace aunty Farah na dashi ranar, shi likitane, likitan ma dayake karatu akan matsalolin mata. Amma sam baiga wani alamomin mai ciki tattare da Aunty Farah ɗinba. Anya kuwa Yayanmu da Aunty Farah babu wani abu da suke ayanzu yake ƙoƙarin bayyana kansa da kansa?...........✍
_Sannu-sannu bata hana zuwa, sai dai a daɗe ba'ajeba. Naga wasu sun ƙagara susan yanda aka samu little da zuwan Zinneerah aikatau, karku damu zaku sani, dan kowane al'amari da muhallinsa yake tafiya, idan kuma gaggawa ta shigo sai ya koma ba'akan tsarin dazai birgeba, wata ranama labarin zamu gama baki ɗaya insha ALLAH. Kudaiyi tattalin man kanku karya tsiyaye, al'amarin mai saukine😂. Ina gaisuwa irin trillions ɗin nan.☺️🤝🏻._
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
[10/14, 5:03 PM] Mom Farooq: *_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_______________________
*Page 46*
.........Koda akazo yin breakfast yau gaba ɗaya gidan aka haɗu harsu Momie domin nuna murnar dawowar Hajiya iya. Aiko taji matuƙar jin daɗi dan bakinta yaƙi rufuwa. Little na jikinta tana bashi da kanta. Ita Zinneerah ma har mamakin yanda ya saki jiki da kowa takeyi, gashi yanzu ta fahimci dai yana neman zama ɗan gidan. Har ranta tanajin daɗin yanda kowa bai taɓa gano alaƙarta da little ɗinba. Amma idan ta tuna randa zasu iya sanin abin na damunta da sakata a fargaba.
Tunda ta zauna bata yarda ta kalli inda AK yake ba, dan ta samu ta ɗan maƙale ne jikin aunty Safiyya ba sosai ake iya ganinta kamar kowa ba. Garama Huzaifa da yazo zai zauna sai da ya tsokaneta. Murmushi kawai tayi dan ita kam ba iya irin wannan wasan tayiba saboda miskilancin ta. Shima dai ya fahimci miskilarce, hakan ya sashi faɗin, “Like Husband like wife”.
Murmushi su Baffah duk sukayi, yaran kuwa kowa yay ƙasa da kai yana gumtse dariya. Ita dai Zinneerah ba sanin inda ya dosa tai ba. AK kuwa yi yayi kamarma baiji mi Huzaifa ya faɗaba, ya maida hankali gacin abincinsa kawai dan hajiya iya ta riga tai musu sabon idan suka zauna gaban abinci shi kaɗai suke bama dukan nutsuwarsu har sai sun kammala.
Shine farkon tashi, kamar an tsikari little shima ya miƙe daga jikin hajiya iya yana faɗin, “Abbana zanje”.
Yanda yay zaram ɗin ya miƙe da maganar tasa data fita raɗam ya saka kowa yin dariya, banda Zinneerah da aranta take raya (kajimin yaro da shegen ɗafa, wai Abbana).
AK kam dawowa yay da baya yasa hannu ya ɗaukesa yana murmushi, ba komai kesa little na ƙara manne masaba sai yawon da yake fita da shi, shiko yaro dama akwai son yawo shiyyasa duk inda sukaga maza koda basu da wayo suke maƙale musu. Balle little dake da wayo masha ALLAH.
“Sweetheart kaima fa ka iya yawo na lura”. AK ya faɗa lokacin da suke nufar ɗakinsa shi da little.
Mommy dake binsu da kallo ita da Baffah tace, “Ƙuruciyar little tamkar Adnan, har wayon tsiyar ya kwaso bai rageba. Wani irin bugawa ƙirjin Zinneerah yayi a take, har takai ta ɗago ta kalli Mommy batare data saniba. Haɗa ido sukai da Hajiya iya dake kallonta cike da nazari ita, tai saurin maida kanta ƙasa. Harga ALLAH maganar ta daketa shiyyasa duk abincinma ya fita mata a rai.
Ganin yanda taketa faman juya cokali a cikin abincin Hajiya iya tace, “Inno kin ƙoshi ko?”. Da sauri tako ɗaga kanta jin ta samu mafita, kafinma Hajiya iya ta sake cewa wani abu ta miƙe da sauri. Sauran da duk basu san mike faruwaba basu fahimci komaiba. Da wannan damar Zinneerah ta samu ta silale daga wajen ta koma ɗaki.
Tayi zurfi a tunani sosai Hajiya iya ta shigo, harta zauna Zinneerah batasan da zuwantaba, sai da ta gama mata kallon nazari tsaf sannan ta taɓata. Nufashi Zinneerah ta kawo a zabure, sai dai ganin hajiya iya ya sakata sauke ajiyar zuciya da ɗan ƙaƙaro murmushi.
“Granny ashe kin shigo? Bara na ɗauka miki maganinki kisha”. Tai maganar tana ƙoƙarin tashi. Kamo hannunta Granny tayi ta maida ta ta zaunar. Hakan yasa Zinneerah ɗan kallonta. Amma ganin itama kallonta Granny keyi saita maida kanta ƙasa dan kallon ya banbanta da wanda ta sani. “Kamannin Abdul-Mutallab da Moddibo na ruɗaki ko? Muma haka suke ruɗamu a koda yaushe. Sai dai nasan jinine kawai yasa Hauwa'u haifo mai kama da Moddibo”.
Ɗan murmushin yaƙe kawai Zinneerah tayi kanta a ƙasa har yanzu, Hajiya iya taci gaba da magana batare da ta damu da yanayin Zinneerah ɗin ba. “Ki shirya zuwa anjima da yamma hajiya Zulai zatazo ku wuce katsina akwai wani aike da zaku kaimin amma ke da ita kawai zakuje”.
Saurin ɗagowa Zinneerah tai ta kalli Hajiya iyan a karo na farko, dan itafa tama kanta alƙawarin bazata ƙara taka ƙafarta katsina ba saboda tsoron karsu Hajiya su ganta. Duk da a yanzu tafi ƙarfin a ƙara kaita inda aka kaitan, kuma tasan ba gidan yankan kai baneba kamar yanda ƙuruciya ta sata kiran wajen a baya.
Cike da basarwa Hajiya iya tai ɗan dariya, “Oh wai kokin taɓa zuwa Katsina ne Inno?”.
Murya a raunane Zinneerah tace, “Sau ɗaya Granny”.
“Kai, duk da kasancewarki bakatsina? A to karma ki faɗa gaban su Jamal sumiki dariyar Danya kawai kika sani”.
Ƴar dariya tayi saboda yanda hajiya iya tai maganar cike da raha. Batare da tunanin komaiba tace, “Granny ai shima aiki Inna tasa wata mata taje dani nayi bama yawo naje ba”.
“Aiki kuma? Kina nufin aikatau fa kenan?”.
A take damuwa ta bayyana akan fuskar Zinneerah, ƙwalla suka ciko mata idanu, murya a raunane tace, “Eh aikatau Granny, ni bansan miyasa Inna bata sonaba. Dagafa wata ƙawarta tazo ta bata labarin kuɗin da ake samu shikenan tasa na bita ko baba bai saniba. Amma tsabar sharri dana dawo sai tace wai yawon banza naje, wlhy kuma ba yawo najeba”.
“Toke miyasa baki faɗama Babanki gaskiyar abinda ya faruba?”.
“Haka kawai naji inajin tsoro Granny, koma nayi niyyar faɗa masa saina kasa dan Baba tsoron Inna yakeji saboda masifarta wlhy, bama shi kaɗaiba ƴan garinmu da yawa tsoronta sukeji dan jarababbiyace sosai”.
“Kai wannan mata ALLAH ya wadaran halinta, ina daɗi ace miji na tsoronka. To amma ke miya faru har tasa aka tafi dake aikatau babu wanda ya sani, harma ta samu damar miki sharri kinje yawo?”.
Hannu Zinneerah tasa ta share hawayenta daketa sakkowa saboda tuna a yanda tabar Danya wancan lokacin, babu wani tunanin wayon manya Hajiya iya ke mata ta fara zayyana mata yanda abin ya kasance.
“Hajja lanti ƙawar inna ce sosai, dan nidai tare na sansu tunda na fara wayo, dan Hajja Lanti dillaliyace a garinmu, tana kuma saida abubuwa iri-iri. Daga baya kuma ta koma ɗaukar yara tana kaiwa aikatau a birni. Hajja lanti ba sona takeba itama, shiyyasa bana murna da zuwanta gidanmu, dan duk randa tazo da wahala kaga harta tafi Inna bata dakeniba saboda tsaban iya haɗa gulmanta. A wata ranar asabar na dawo daga tallan gyaɗa da riɗi a gajiye na iskesu zaune a tsakar gidanmu suna magana da ban san kota micece ba. Ni dai na gaidasu na bama Inna kuɗin tallar na shige ɗaki dan tace karna sake zama a tsakar gida idan tayi baƙi. Ban jima da shiga ba ta ƙwalamin kira. Koda na fito sai da suka gama min kallo na wani lokaci ne naji hajja Lantin na cewa “Ai wannan ma itace dai-dai a yanzu. Dan za'a jima ana samu tattare da ita”. Bansan ina zancen nasu ya dosaba. Ni dai Inna tacemin naje na canja kaya nawuce can bakin ɗorawar kan hanya na jira Hajja Lanti zamuje anguwa. Ban musa mataba naje na canja kayana na fito, saita sake korani da cewar naje na saka kayan sallata. Zuwa nai na sake canjo kayan na fito, a gabansu na tafi inda tace naje na jira hajja Lanti ɗin. Na jima a bakin ɗorawa zaune sannan hajja lanti tazo ita da wasu yara da ban sansu ba. Batare da itama tamin bayaniba ta bani hijjabi da nikab wai na saka. Nidai ban musa mataba na saka. bayan na sakane ta kira masu mashin su uku suka daukemu zuwa Gozarki. A Gozarki muka kwana dan maraice ya rufa lokacin. Washe gari tunda farar safiya muka tafi inda ake hawa mota muka shiga motar Katsina da naji ana faɗi a wajen. Nasha mamaki amma a raina ina ɗoki zanje katsina da nakeji a labari. Koda muka isa Katsina an saukemu a wani waje mai tarin jama'a, mudai muka shiɗa a motar kamar yanda tace mana. Daga nan an ɗibemu a napep zuwa wani waje da naji hajja Lanti ta kira da suna anguwar yari.
Kamar yanda ƴan uwan tafiyata basa gane komai a wannan tafiya nima dai ba ganewa nakeba. Sai dai ina lure da komai da akeyi. Kamar sunayen wajajen da muka sauka da inda muke tafiya. Mun isa anguwar yari da tace a kaimu. Inda aka saukemu a wani gida mai matsakaicin ƙyau da girma.
Koda muka shiga cikin gidan mun samu kusan mutane goma a cikinsa, Sai wata dattijuwar mata da tafi hajja Lanti shekaru dajin daɗi. Yanda ta tarbemu ne yasa naji ɗan dadi ga raina. Sai dai yanda maza da mata ke shiga da fita gidan baiminba a rai. Mun jima zaune suna hira kafin a kawo mana abinci muci, bayan mun koshi aka haɗamu da wata a gidan mai suna Sadiya. Itace ta kaimu wani ɗaki wai anan zamu zauna. Nidai kallon kowa nake da mamaki da tunanin mi mukazoyi nan? Miyasa Inna tace na biyo wannan matar nan batare da Baba ma ya sani ba?. Banda mai bani amsa, shiyyasa naja bakina na tsuke. Daga wannan lokaci ban sake ganin hajja Lanti ba a gidan, ban kawo komai a rainaba sai tunanin ko taje wani wajene ta dawo tazo mu dawo gida. Amma sai naji shiru har tsayin kwana biyu. Duk da ana bamu abinci muci mu ƙoshi, ga television muna kallo hakan baisa hankalina ya kwantaba, sai dai inajin tsoron na tambayi wani ina hajja Lanti take?. A randa muka cika kwanaki uku a gidan naga an kwashi abokan tafiyata su uku aka fita dasu a gidan, daga haka ban sake ganinsuba suma. Hankalina ya tashi na shiga yi musu kuka akan nidai su maidani garinmu, danni na ɗauka kodai ƴan yankan kai ne ma. Ranar naga ruwan masifa wajen matar nan, dan kamar zata dakani a turmi saboda masufar data dinga min. Dolena shanye kukana saboda tsoronta. Da maraice aka sake kwashe sauran abokan tafiyata su biyu da suka rage aka barni ni kaɗai sai waɗanda na samu a gidan. Ranarma nayi kuka har takaini gayin masassara.
Magani kawai suka bani nasha, daga haka babu wanda ya sake bi takaina, sai ma da daddare kusan ƙarfe takwas hajiyar tace a tasoni zamu fita. Ina jinta daga ɗaki danba barci nakeba, tunanin asibiti zata kaini yasa ban kawo komai a rainaba na tashi na fito bayan na saka hijjab ɗina. Tsaye na sameta a tsakar gida cikin gayu, na gaisheta jikina duk a sanyaye saboda zazzaɓi dake cina. Gaba tai na bita baya batare damin maganaba. Muna fitowa ƙofar gida muka iske mota mai ƙyau.
Motarnan muka shiga, gabana nata faɗuwa nidai inata tunanin lokacin yanke nawa kan yayi. Dan haka naita addu'a kala-kala ina sharar hawaye a ɓoye da roƙon gafarar babana a zuciya, a haka muka iso wata babbar anguwa dabansan sunantaba, sai dai yanda ko'ina ke ƙwanyar da hasken lantarki zai tabbatar maka da anguwar masu kuɗice. Katafaren gida mai blue gate aka buɗe mana muka shiga, kasancewar darene bazan iya banbance tsarin gidanba, sai dai lallai ya haɗu matuƙa. Koda muka fito a motar hajiya ce ta kama hannuna muka shiga ciki. Anan ne na sake tabbatar da gidan ya haɗu, masu shi kuma sunada kuɗi.
Waɗanda muka samu a falon ne sukai mana iso zuwa ciki bayan mun gaisa, an sake kaimu wani falon, inda muka zauna zaman jiran matar gidan. Munfi ƙarfin awa ɗaya zaune kafin ta fito, ƙyaƙyƙyawa ce sosai baƙa, daka ganta kaga bafulatanar bakatsiniya, dan ƙyawun nata ya fita sosai masha ALLAH. Sai da ta gama mana kallon tsaf kafin ta amsa mana gaisuwa tana sake ƙaremin kallo, cikin maganar daban ganeba hajiya tace, “Ranki ya daɗe ga wata ki duba ko zata iya, yau kwana uku da kawomin su daga wani ƙauye”.
Kallona ta sakeyi sama da ƙasa tana ɗan yamutsa fusaka. Ta ɗage kafaɗunta cike da isa tana faɗin, “Uhm babu laifi kam, dan tafi waccan komai, girma kawai waccan zata fita. Amma ina zuwa”. Tai maganar tana miƙewa, fita tai, babu jimawa sai gata ta dawo ɗauke da waya, batare da tayimana maganaba ta shiga haskani da hasken wayarta daban fahimci ma'anarsaba a wancan karon, sai dai a yanzu inaji a raina camara ne. Bayan ta gama kuma ta fara waya, da turanci take magana shiyyasa banji komaiba, bansan dai ga hajiya ba. Ta ɗauki lokaci mai tsaho tanayi kafin ta ajiye ta dubi hajiyar, “Ba damuwa zamu gwada mu gani, bara na ɗakko miki sauran saƙonki ko, idan akwai wani matsala zan nemiki daga baya kafin ki wuce, namafison sai mun kammala komai mun fara wucewa kafin taki tafiya”.
Baki a washe Hajiya tace, “Ato babu damuwa ranki ya daɗe, ni bani da matsala duk yanda kukeso sai ayi, fatana dai ALLAH yasa a dace akumayi nasara”.
Cike da yanga ta amsa da amin. Daga haka taje ta kawo mata saƙon da tace. Inaji ina gani hajiya ta miƙe tana faɗamin aini nan zata barni, nanne zanyi nawa aikin, dan haka sai nayi biyayya, yi nayi bari na bari.
Sosai na fara hawayen fili saɓanin na zuci, yanda zuciyata kemin zugi da zafi ya hanani yin magana harta fice ta tafi bayan ta bani ɗari biyar a kuɗin danaga an bata masu yawa, itama haijiyar gidan ta shige batare damin maganaba. Da wannan damar nai zaman kuka na kusan awa ɗaya kafin wata tazo cikin wanda muka fara tararwa a falon farko ta kama hannuna muka fice.
In taƙaita miki Granny tun daga ranar zazzaɓina ya ƙaru, inaga ganin yanda nake galabaita yasa Hajiyarnan ɗaukata a washe gari takaini wani asibiti mai ƙyau da alama na kuɗine. Anan aka bani gado. Sosai likitan yaytamin tambayoyi harnaji nama ƙosa dashi, amma na daure dan lafiyata nake nema ai. Kwanana shidda a asibitin nan na warke sarai aka sallamoni, sai dai kuma hajiya ta kaini wani gida ba nata da aka fara kainiba, naji tsoro sosai, dan can babu kowa sai wata dattijiwar mata mai suna Harirah.
Ɗaki guda aka bani a gidan, wanda yaji duka kayan more rayuwa, ni harma abin ya ban mamaki amma sai ban tambayaba tunda dai ance aiki nazoyi. Komai na nema ina samu a gidan, amma sai dai a tsorace nake, dan haka kawai na kasa yarda da sakin jiki da baba harirah, sai dai kullum sai ta shigo ɗakina ita ta sakani shan magungunana na asibiti da aka bani. Hajiyar kuma ban sake ganintaba sai bayan kwanaki sai gata. Cataimin na shirya muje asibiti likita ya sake dubani, ban kawo komai a raiba na shirya na bita zuciyata fal fargaba. Munje likita ya sakemin gwaje-gwaje, sai yace wai akwai wani ciwo dake damuna zasu ban magani. Daga wannan maganar aka kaini wani ɗaki, tunda akaimin wata allura ban sake sanin inda nakeba sai a gida. Ni kuma tunda na farka sai tsoro ya kamani ganin ko baba harirah ɗinma yanzu babu, sai wani gardi abin tsoro dake a waje. Hankalina ya tashi, da ƙyar na samu nai wanka nayi salla. ina idarwa na saka kayan danazo dasu daga gidan hajiyar farko da aka kaini, ALLAH ya taimakeni na silalo na fito daga gidan, ɗari biyar ɗin da hajiyar ta bani da zata tafi lokacin data kaini can gidan itace ta taimaka mani na koma Danya. Koda na koma kuma saina kasa bama kowa labarin abinda ya faru har Babana, duk da inason na faɗa masa kodan kalmar iskanci da Inna ke dangantani da shi sai dai inajin tsorone”.
Shiru hajiya iya kawai tai tana kallon Zinneerah kamar mai karanto komai akan fuskarta, sai dai wani irin tausayin yarinyar da ƙaunarta na sake shigarta. Dan yanda take bata labarin a nutse sai take ƙara godema ALLAH da samunta matsayin matar jikanta mafi soyuwa a ranta. Ta ɗan murmusa cike da basarwa tana faɗin, “Uhmm lallai dole ki kasa mantawa da birnin katsina. To amma ita hajiyar data kaiki gidan baki koma gidantaba bayan kin baro can?”.
“Wai Granny sokike na koma ta sake maidani, nifa wlhy haka kawai naji banason hajiyarnan data kaini asibiti, ta cika tsare gida da mulkin tsiya kamar sarki”.
A karon farko Hajiya iya tai dariya da juyawa tana kallon AK datun fara maganarta da Zinneerah ya shigo ɗakin, sai dai jin labarin da Zinneerah ta fara badawa ya sakashi dakatawa batare daya shigoba. Yanda ya kafe Zinneerah da idanu yana ma labarin nata fashin baƙi da nazartarsa yasa hajiya iya faɗin, “Amma baki taɓa gamo da maikama da wancan mutumin a katsina ɗinba?”.
Sai a lokacin Zinneerah ta farga da AK, duk da ta jima tanajin ƙamshinsa a hancinta bata kawo shi baneba. Kallo ɗaya tai masa tai saurin maida kanta ƙasa saboda yanda kwarjininsa ke cika mata idanu da zuciya. Cikin girgiza kai tace, “A'a Granny, anan na fara ganinsa nikam”.
“Inno bafa wasa nakeba”.
Da iya gaskiyarta tace, “Wlhy kuwa Granny”.
Hajiya iya zata sake magana AK ya katseta da faɗin, “Kin shirya ne na kaiki gidan Gwaggon?”. (mmn sadiq).
Tsaf hajiya iya ta fahimci dalilinsa na katseta, dan haka tai guntun murmushi da cewa, “Eh bara na kimtsa, ai hada Inno ma zamuje saimu barta acan dan da safe idan ALLAH ya kaimu zata dawo akwai inda zan turata”.
Baice komaiba sai duban Zinneerah ɗin datai ƙasa da kanta yaɗanyi, ya ɗauke idanunsa ya juya ya fice.
Binsa da kallo Zinneerah tayi, tana ganin ya fice ta sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya da har sai da hajiya iya tai murmushi.............✍
*_ZAFAFA BIYAR NEXT LEVEL sunzo da sabon salon da duk ya zarta na baya_*
Dan haka masoya karku bari ayi tafiyar bana babu ku a ciki💃🏻💃🏻.
*_★ AL-ƘIBLA_*💘
_Na Safiyya Huguma_
*_★ MABUƊIN ZUCIYA_*💖
_Hafsat Rano_
*_★ DALAAL_*💝
_Na Miss xoxo_
*_★ UBAYD MALEEK_*💓
_Na Mamu gee_
*_★ MAKAUNIYAR ƘADDARA_*💔
_Na Bilyn Abdull_
Lalai daga ji babu tambaya bana ma ZAFAFAN ku da turirinsu suke tafe. Dan dagani kasan za'a ragargaza cakwakiya, soyayya. Tare da nishaɗi💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻.
Gasu duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
0903 234 5899
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
*_ALLAH ka gafartama Iyayenmu🙏🏻😭_*
[10/14, 5:03 PM] Mom Farooq: *_TYPING📲_*
*_LIttafin nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH karki karanta sai kin biya. Idan kuma kin saya, muna haɗaki da ALLAH karki fitar mana. Dan ALLAH ku zama masu riƙon amana da adalci a garemu🙏🏻😢_*
_________________________
*Page 47*
...........Cike da ɗokin zuwa ganin mmn sadiq dasu Aliyu Zinneerah ta shirya cikin wando da riga na parkistan red and white, sai gyale red data naɗa a kanta wanda ya fiddo mata ƙyawun da fuskrta ta ƙara. Kayan sun zauna mata ɗas a jiki kasancewarta mace mai mulmulallan jiki da ƙyawun surarta ta ƙuruciya. Babu wani kwalliya a fuskarta, amma ta saka lipstick kaɗan da yayma lips ɗinta ƙyau, dan tanada lips masu ƙyau da tsarinsu ya fita sosai yanda suke ɗaukar jambaki kamar wata babyn roba. Takalmi tasa mai ɗan tudu da igiya, sai side bag ɗinta ƙarama. A yanda tai ƙyau dolene ka kalleta ka sake kallo, ga ƙamshi tana bazawa dan Zinneerah gwanace wajen ɓarnar turare, idan ta samu batai masa da sauƙi. Ƴar jikkar data zuba kayanta kala biyu da tsarabar chocolates ɗin su Abdul ta ɗauka, dama hajiya iya ta fice ita tana falo tuni.
Hajiya iya kawai ta samu a falon itama tana ƙoƙarin fita, samarin gidan tun bayan breakfast suka fice, hakama ƴammatan, su Jamal kuwa batasan ina suka dosaba. Hajiya iya dake ƙoƙarin fita tace, “Inno kashe tvn nan ki taho nasan Moddibo nacan ya cika da hasahinmu”.
Da to Zinneerah ta amsa tana ɗaukar remote, bayan ta kashe tvn ta gyara labulolin sannan ta fito, ƙofar ta rufe dan masu aikin Hajiya iya basu dawoba, maybe sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Tafiya ta fara cikin nutauwarta tana ƙoƙarin ɗaura agogo data ɗakko a tsintsiyar hannunta da dosar inda ta hango Hajiya iya da Mommy tsaye da alama harda ita zasuje. Idonta bai lura da AK ba sai da tazo dab dasu tana ɗagowa da shi ta fara tozali yana ɓullowa daga ta gaban motar waya a kunnensa alamar magana yakeyi.
Kallon nata yayi dai-dai da saukar nasa idanun a kanta. A take ƴar sakewar data hango akan fuskar tasa ta ɓace ɓat, ya tsuke fuska yana mata kallon data nema kifawa saboda harɗewa da ƙafafunta suka shigayi. Saurin maida kanta tai ƙasa tana cigaba da takowa ranta fal nauyinsa da kwarjini, sai mita take a ranta kuwa. (Haka kawai bakama mutum komaiba yayta hararka, shi wai baya ganin waɗanan idanun nasa manya da ƙarfinsu yay yawa suna tsorata mutane).......
Da wannan tunanin ta ƙaraso Mommy dake kallonta tana ambaton, “Masha ALLAH ɗiyata irin wannan ƙyau haka”.
Ƙasa Zinneerah ta ƙarayi da kanta tana murmushi, hakama Hajiya iya murmushi take tana kallonta itama. A bazata sukaji AK ya saki tsaki, cikin faɗa-faɗa yace, “K! Koma kisa hijjab”.
Ba Zinneerah ba hatta su Mommy sai da suka dubesa, shiko ya fuske ya buɗe murfin motar ma a fusace ya shige abinsa. A sanyaye Zinneerah ta juya zata koma dan shi ba abin wasanta bane, waɗandama suka girmeta da shekaru masu yawa a gidan sunabin dukkan dokarsa balle ita ƴar jiya. Dakatar da ita Hajiya iya tayi ganin yanda tai ƙwalƙwal da idanu kamar zatai kuka, ta kamo hanunta tana matsawa saitin driver da yake zaune. “Haba Moddibo aimata haƙuri tunda ta rigada ta fito, ai kaga gyalen ya rufe mata jiki, kuma naga daga mota sai gida”.
Shiru yay kamar baiji mi Granny ta fadaba, sai da ta ƙara leƙasa tana faɗin, “Oh nima yarfin daka iya zakamin?”.
Idanunsa da suka canja launi ya ɗago ya dubi Hajiya iyan, “Amma Granny .......”
“Dan ALLAH ai nace”. Tai saurin katsesa dan tasan shegen taurin kansa da dagiya akan abinda duk ya kafama sharaɗi. Badan yasoba ya ɗauke kai daga kallonta yan yima motar key. Murmushi Hajiya iya tayi da duban Zinneerah. “Kinga zagaya can kusa dashi ki zauna Inno, mu saimu zauna baya da Mommynku”.
Kamar Zinneerah ta fasa ihu taji, dan yanda taga fuskarsa batai zaton ya haƙuraba, kawai dai yayi shirune dan Granny ɗin. Amma yata iya, dole ta zagaya tabi umarni. Zama tai maƙure jikin murfin mota, zuciyarta na mata hasashen ko ina little yake? Dan tayi tsammanin dashi zasuje itakam. Yanda AK ya figa motar da ɗan ƙarfi yasata saurin dubansa, sai dai da sauri ta ɗauke idonta ganin wani shegen harara daya watso mata laɓɓansa na motsawa tamkar mai magana komai son cewa wani abu amma ya gagara furtawa.
“Kai malam wlhy karka zubar damu, dan idan ka kasheni banga sake ganin ɗan inno ba ALLAH ya isa mai kishin tsiya”. Hajiya iya ta faɗa da iya gaskiyarta tana zazzagama AK masifa. Dariya Mommy ta sanya ganin yanda AK ɗin ya hararo Hajiya iya ta mirror.
Zinneerah kanta sai da zancen hajiya iya ya bata dariya, amma sai tai murmushi kawai tana kauda kanta gefe, dan zuwa yanzu ta fahimci Yayansu da Granny ba'a haɗuwa ba'ai faɗa ba. Kuma itace mai takalar faɗan shi kuma yayta mazurai, idan kuma ya magantu ya rama sau ɗaya yay mata banza.
A nutse yake tuƙin cike da ƙwarewa da bin dokoki, sai da suka hau titi sosai ya fara amsama Mommy maganar da take masa daga can baya, hajiya iya na tayata. Zinneerah dai bakinta gum, sai strawberry sweet ɗin dake bakinta take ta faman juyawa tana kallon hanya, tana jiran taji ya tambayeta ina suka dosa taga ya ɗau hanyar anguwar kai tsaye. Mamakine ya kamata sai dai babu damar magana, sunyi kusan rabin tafiya taga ya gangara dasu wani super market, sai da ya samu waje yay fakin sannan yay magana batare da ya kalli kowa a cikinsu ba. “Mommy muna zuwa Please”.
Cike dajin daɗi tace, “A fito lafiya”.
Hajiya iya kam baki ta taɓe da ɗauke kai tana maganar da su dake gaba ba jinta sukeba. “Muje”. Ya faɗa yana buɗe murfin ya fice. Zinneerah bata fahimci da ita yakeba sai da Mommy tace, “Ɗiyata fita kuje ku dawo kinji”.
Sai da Zinni taɗan waro idanunta waje, tace, “Mommy amma.....”
“Maza kije karyayi faɗa”.
Mommy ta katseta kafinma tace komai. Dole Zinneerah ta yunƙura ta fita zuciyarta na dukan goma-goma. Idanunta kuwa harsun tara ruwa. Ina ita ina shiga irin wannan wajen da Yayansu, itakam yau tana cikin abba-tuwa, shikenan ya samu damar dazai cimata uwa akan ƙin bin maganarsa na saka hijjab duk da Granny ce tai bell nata dai.
Koda ta fito da birkitattun idanunsa ta fara cin karo, ga fuskarnan kamar zatai aman abinda kecin ransa. Ƙasa tai da kanta tana ƙoƙarin haɗiye rauninta dake son bayyana. Ta fiske abinta da takowa inda yake a hankali batare data sake yarda sun haɗa ido ba. Tana isowa wajen ya miƙa mata handkerchief ɗin hannunsa, “Kwashe wannan abun na bakinki”.
Idanunta dake tara ruwan hawaye ta ɗago ta kallesa. ya zuba mata hararar data sakata amsar handky ɗin babu shiri, cikin ɗan tura baki ta fara kwashe ɗan janbakin dabai taka kara ya karya ba. Handky ɗin ta miƙa masa tana ƙoƙarin haɗiye kukanta. Batare daya amsaba ya raɓata zai wuce da faɗin, “Idan baki shiga hankalinki da saka wannan janbakin ba saina tsinke waɗanan lips ɗin da haƙori mtsoww”.
Duk yanda Zinneerah taso daurewa kasawa tai sai da ta bisa da kallo mamaki ƙarara akan fuskarta. Ganin bata biyosaba ya sakashi tsayawa cak. Da sauri ta nufesa saboda fahimtar dan ita ɗin ya dakata. Jerawa sukai a tare gwanin sha'awa, dan yanda yake tafiya babu garaje haka itama take tafiyar, amma kasancewar abinda ya faru tana tsoron sake laifi ya ƙara hanzarta tata tafiyar, sai suka samu daidaito dashi dan ya fita kuzari da tsaho.
Shigarsu wajen ya sake bayyana ɓacin ransa a saman fuska ganin yanda mutane ke ɗan kallonsu jefi-jefi, a bazata kawai taji ya ruƙo hannunta cikin nasa mai taushi da ƙamshi tamkar nata ɗinma, dan zuwa yanzu ta fahimci jin daɗi ke kawo irin wannan baiwar ga fata bawai shafe-shafe ba. A kusan tare ita da shi suka lumshe idanu saboda jin sabon al'amarin dake saukar musu a gangar jiki da magudanar jini, ya sake damƙe hannun da ƙyau yana ƙoƙarin dai-daita kansa gudun kar ayi abin kunya.
Zinneerah kam ai murus bakinta ya ƙara mutuwa sai sama da ƙasa da numfashinta keyi tana ƙoƙarin fisgosa da ƙyar. Haka tanaji tana gani ya shiga zagayawa dasu yana ɗaukar abubuwa da sakawa a basket ɗin da ɗaya a ma'aikatan wajen ke biye dasu da shi. Itama kuma sai yanda budurwar ke kwarkwasa da wani iyayi a gaban Yayan nasu ya bama Zinneerah haushi ta shiga hararta ta gefen ido tana faman yamutse fuska.
AK bai fahimci halin da take ciki ba sai da sukazo wajen biyan kuɗi, har lokacin yana riƙe da hannunta tamkar ance za'a ƙwace. ATM ya ciro a aljihun wandon getzner shaddarsa ash zai miƙa budurwar data tayasu takai hannu zata amsa cike da yauƙi, caraf Zinneerah ta kawo hannu ta amsa daga hannunsa tana wani juya ido da sake miskile fuska.
Yanda tai ɗin ya saka wata dake kusa dasu kwashewa da dariya ita da ƙawarta. A fili tace, “Wlhy yarinya kin birgeni, adana abinki kar ƴan shishshigi suyi miki wuff da shi”.
Sarai Zinneerah ta jita, amma sai ko kallon inda suke bataiba tama ɗauke kai gefe. AK ma da sarai yajisu bai nuna yajiba, sai dai ya ɗan dubi Zinneerah ta gefen ido maganar ƴammatan na masa kaikawo a zuciya da ƙwaƙwalwa.
Koda aka gama saka musu a leda budurwar bata daddaraba duk da yarfatan da ƙawayenta sukayi da Zinneerah ta sake kai hannu zata ɗauka ledar Zinneerah ta rigata ɗauka da faɗin, “Don't worry, thanks”.
Kasa haƙuri AK yayi yanzu kam sai da ya ɗan dubeta, mi zuciyarsa ta ayyana masa oho sai gashi da sakin wani malalacin murmushi yana sake damƙe hannunta dake cikin nasa, daga haka ya jata suka fito yana mamakin miskilancinta da kame kai tamkar ba ƙaramar yarinya ba.
Zinneerah na ganin sun fito ta fara ƙoƙarin zame hannunta a nasa, shima babu musu ya saki tare dayin gaba abinsa. Sai dai kuma abinda sukema gudun su Granny, kuma sun gani. Dan Granny dake bama Mommy labarin da Zinneerah ta bata akan zuwanta katsina aikatau tun bayan fitarsuce ta fara hangosu. Ta taɓa Mommy tana faɗin, “Auta kalla mutanenki”.
Ɗago kan Mommy yayi dai-dai da sakin hannun juna da sukayi, dan haka ta murmushi kawai da faɗin, “Inna tarkon nan naki fa mai ƙarfine, dan na ƙaramin damƙa yayma ɗana ba, yana dai ƙoƙarin nuna halin nasa na basarwa ne”.
Baki Hajiya ita ta taɓe da cewa, “Ai sai yayma ubanda baisan halinsaba. Ni tuni na harbosa ai. Itace dai na kasa gane kanta dan itama gidan miskilancince, bansan yanda gidan nasu zai kasanceba an tara masu shegen baƙin rai da miskilanci. Shiyyasa banason a faɗa mata har sai ta tare suje can su ƙarata”.
Dariya Mommy ta sanya har su Zinneerah suka iso wajen, sai da suka shigo mota ta haɗiye abinta tana musu sannu. Duk amsawa sukai yana tada motar, daga haka sai gidan mmn sadiq da Zinneerah taita mamakin tayaya ya sani?.
★★
Tarba suka samu maiban mamaki daga mmn sadiq da maman halima. ashe hajiya iya ta sanar musu da zuwan nasu, shiyyasa mmn sadiq datai niyyar zuwa dubata yau dole ta haƙura. Zinneerah kam ai tuni ta faɗa jikin mmn sadig tana murnar ganinta ita da mmn halima. hakan datai har sai da ya bama AK mamaki dan baiyi zatonta hakaba. Kasancewar Abba na gida yana jiransu a falonsa aka sauke AK, su Hajiya iya kuwa da mmn sadiq keji kamar ta goya suna a sashenta.
Duk yanda mmn sakina taso nuna halin nata garesu saita kasa. Dan wani cika mata ido sukai dole ta kama kanta harda zuwa ɗakin mmn sadiq gaishesu. Ai kam sun amsa mata da fara'a da mutuntawa, hakan da sukai kuma sai ya ƙara musu kima a idonta da shakka. Mmn halima ma cike da girmamawa tazo ta gaidasu, Hajiya iya nata sanya mata albarka dan bata manta da fuskartaba taje mata gaiauwar Inno.
Saboda zuwa nan hajiya iya dama taƙi cin abinci, dan ta taho da shirin cin abincin gidan ɗiyar tata. Aiko taji daɗin samun masa da mmn sadiq tai musu, sai gashi daga ita har Mommy sunci sosai suna godiya. hakan yasa Mmn sadiq ƙara jin daɗi da nutsuwa. Dan koba komai ai sun bata kimarta. Zinneerah kam tuni tana sashen mmn halima ta barsu dan su sake da kuma kasancewarsu manya a gareta.
Da wannan damar mmn sadiq da baƙinta sukai hirar zuminci da tattaunawa game da labarin da Zinneerah ta bama hajiya iya da kuma abinda ya faru akan zancen little da maganar ɗaurin aurenta. Harma da shirye-shiryen tariya da a take mommy ta tabatar musu ita ta gama shirya komai rana kawai suke jira insha ALLAHU.
Hawaye sosai mmn sadiq keyi har sai da hajiya iya ta shiga lallashinta.
Sai da akai sallar la'asar Abba ya shigo gaida su hajiya iya tare da AK da shima yaci masa sosai dan yana sonta, ya kuma sha zoɓo shima. Sun gaisa cikin mutunta juna, suka ɗan ƙara tattaunawa har zuwa kusan biyar da rabi sannan sukai haramar tafiya.
Sai kuma ga Zinneerah tai ƙwalkwal da idanu na kewar hajiya iya da zatayi duk da dai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu zata koma. Sau biyu suna haɗa ido da AK da tuni ya shige mota ta mirror ɗin waje, daga ƙarshe dai ta matsa daga saitinsa tana ɗaga musu hannu.
Tafiyarsu da mintuna basufi talatinba su Sadiq suka dawo gida. Ganin Zinneerah suka haukace da murna suna tambayarya ina little ɗinsu?, su dai sunyi kewarsa dan ALLAH a dawo musu da abinsu. Dariya kawai take musu dan ita dai wannan ba huruminta baneba ai. Tunda batasan yaje canba itama ganinsa tayi.
Bata samu zama da mahaifiyartaba sai dare bayan yaran sunyi barci, kasancewar ɗakin mmn sadiq ɗin zata kwana suka sami damar yin hira, yayinda mmn sadiq ketama ƴar tata nasiha a kaikaice akan aure da muhimmancinsa da darajojinsa. Ita dai Zinneerah saurarenta kawai takeyi bawai fahimtar dalilin yinsuba. Sai dai suna shiga kwakwalwarta tana kuma ƙoƙarin adanawa da fatan yin aiki dasu a duk sanda ƙaddara ta tilasta mata yin aure dan bata kawosa a lissafinta sam. ita kullum lissafi da budget ɗinta akan karatune mai zurfi kawai.
Washe gari ma bayan tafiyar su Abdul skull sake zaman hira tayi da mamanta. A yau ɗinma hirar ta kasance kusan duk nasiha da dabarun zaman gidan aure koda da kishiya. Harma dai takai abin ya fara bama Zinneerah mamaki amma saita danne a ranta kawai.
Karfe huɗu dai-dai sai ga Ni'ima da driver sunzo ɗaukarta, jitai kamar ta fasa kuka. Amma jin mmn sadiq tace zasuje taron biki Danya kuma harda ita nanda kwanaki tara yasa taɗanji daɗi a ranta har fuskarta ta nuna. Bayan ta gama matse-matsen hawayenta ta shirya suka wuce ɗauke da madaidaicin botikin gullisuwa da mmn sadiq ɗin tai musu.
Koda suka iso gidan cike da murna suka tari juna dasu Bahijja daketa mata ƙorafin basusan zataje wajen mama ba da sun bita. dan sai da su Mommy suka dawo suka sani. Haƙuri ta basu kawai, daga haka suka shiga hidimar cin gwullisuwa kuma.
Ana idar da sallar magrib hajiya iya tai baƙuwa. Bayan sun shiga ɗaki kusan awa ɗaya aka kira Zinneerah, kai tsaye hajiya iya tace mata ta shirya zasu tafi da baƙuwar gidanta. Mamaki ya kama Zinneerah, amma ganin yanda hajiya iya ta fiske dole itama ta shanye mamakin nata.
Bayan ta shirya Hajiya iya ta jata gefe tai mata ƴar nasiha da gargaɗin duk abinda akai mata a inda zataje kartai jayayya, karkuma tai wasa wajen koyon komai ɗin. Ta amsama hajiya iya da girmamawa ita dai tana matsar ƙwalla, dan hankalinta ya tashi jin wai sati ɗaya zatai acan, a hakanma hajiya fadi take waje ya ƙure ba haka tasoba.
Zinneerah naji na gani ta tafi tabar su Meenal tana hawaye suma sunayi tamkar masu rabuwa har abada. Hajiya iya kanta sai da taji kewarta, to amma wannan shine kawai gatan da zatai mata ta miƙata wajen kwararrun mata ta fannin sanin gyaran jiki da wasu sirrika irin su hajiya Falmata su gyara mata ƴar jikallen tata. Dan idan tai dubi da abinda ya faru da kuma kishiya irin Farah saita ƙara jin wannan shine gatan.
Koda suka iso gidan hajiya falmata bata tsaya sanyaba saboda gargaɗi da sharuɗɗan hajiya iya akan irin salon gyaran da take buƙata aima Zinneerah ɗin, itako hajiya falmata dama aikinta kawai ta sani batasan wasaba. Musamman ma aiki irin wannan na manyan mutane kamar su hajiya iya da suke alaƙa tun zamanin ƙuruciya ba abinda zatai sanya bane. Dan haka tun a ranar ta fara gyara Zinneerah daga isowarsu gidan ko hutawa batama bari sunyi zaman yiba. Tun Zinneerah na kallon abin wani iri hardai ta fara jin yana shiga jikinta da sha'awarsa ganin yanda ta fara canjawa da ƙamshi mai kama jiki da gogewar fata a cikin kwana biyu.
Babu abinda ke damunta sai kewarsu Jamal da hajiya iya dan ko abinci da ake bata na musamman ne. Hajiya Falmata kuwa nata aikinta da koya mata abubuwa kai tsaye har kunya na neman kashe Zinneerah da ganin hajiya falmata zata iskantar da ita shekarunta basu kai ba. A ranta kuma tana mamaki yanda ake mata magana mai kama da harshen damo akan aure da zamantakewarsa. Ta rasa wannan dalili itakam, takumayi alwashin bazata tambayaba zata cigaba dabi da ido da kuma saurare.
A Ɓangaren su Hajiya iya kuwa Zinneerah na barin gidan aka ware fara tsare-tsaren biki da maganar invitations dan hajiya iya da Baffah fa shiri suke gagarumi kodan ƙular dasu Mammah dake can hotel suna jiran tsammani daga mai bincike, AK kuwa daketa ƙoƙari akan aikin shinkafarsa yana sane dasu, dan tuni yasa aka bincika masa inda suke, ya kuma shirya ɗaukar mataki akan Farah data bijirema maganarsa.
Akan gyaran gidansa kuwa Dr Mahmud da Huzaifa ne tsaye akai duk da gidan bama taɓa zamansa Farah tayiba. Garamashi yankan zauna lokacin da yake shigowa ƙasar a munafunce.
Ranar da Zinneerah ta cika kwanaki huɗu wajen Hajiya falmata lefen da Momie ta haɗa gudunmawarta ya iso, sai kuma ga Adilah da Mahma daga london suma sun iso da nasu kayan lefen, dan AK na sanar da ita komai bai ɓoyeba, takuma bashi goyon baya ɗari bisa ɗari.
Zokaga yanda Adilah ke murna da farin cikin kasancewarta cikin ƴan uwa. mahma kuwa abinci kawai taci anan taɗan huta ta nema inda su Mammah suke, dan bata son ita kanta su san da maganar auren har sai ranar tariyar insha ALLAHU..............✍
0 comments:
Post a Comment