Dr.Bobby kuwa Nur na ajiyeshi a gida ya shige ciki ko sallama bai tsaya sunyi dashi ba...kawai gaba daya jinshi yake wani iri shiba mai lafia ba kuma shi ba mara lafia ba...wanka kawai ya sakeyi ya kwanta amma duk kokarinshi na ganin yayi bacci abun gagaranshi yayi...har su Mummy duka dawo bai runtsa ba...yanajinsu yaji fitowa yasan suma sunyi tunanin yayi bacci shiyasa basu nemeshi ba shi kuma bacci kiri kiri yace bazai daukeshi ba...har dare ya raba bai samu baccin ba haka yayita juyi kan gado yana faman tunanin abunda sam bai shafeshi ba sai can wajen 3 baccin ya lalla6o yayi gaba dashi...rashin samun bacci da wuri yasa ya makara sallahn asuba dan time din daya tashi an idar da sallah sai a gida yayi nashi snn ya sake kwanciya amma still baccin bai daukeshi ta dadin rai ba saida ya gama ja masa aji...can cikin baccin ringing din wayanshi ya tasheshi...a fusace yakai hannu ya dauko wayan yayi sliding yakai kunnenshi ko sunan mai kiran bai tsaya dubawa ba...daga can 6angaren Rayhan tace"uncle bobby"...ya runtse ido yanajin wani irin haushinta na lullu6eshi...yanxu dama duk uban kiran nan da ake jera mishi wnn yarinyar ce?...yana kokarin kashe wayarshi dan yasan yana bude baki mgn zai fada mata mara dadi yaji ta sake cewa"uncle bobby kayi hakuri plss...na kasa hakura ne...jiya Mummy ke cemin kaje wurin dinner kuma har ka tafi ban karaso ba...a wurin make up ne aka 6ata mun lokaci amma naso haduwa dakai sosai"...shiru ya sakeyi yanajin kaman yakai hannu ya kwada mata mari ta cikin wayan..he is just trying to control his temper sbd idan ta kaishi bango bazataji da dadi ba...jin shiru bai still baice komai ba tace"uncle bo..."bata karasa ba ya katseta da fadin"ke hold it plss..how dare u call me at this time of the day?..are u insane?..bakisan safiya bane ko bakisan i might be sleeping ba?.."kwantar da muryanta tayi sosai tace"kayi hakuri dan Allah..naga 8 ya wuce so i taught kana Hospital..am sorry"..tsaki ya saki bayan ya duba wall clock din dakin nashi yaga it's 8:36 dan haka ya kashe wayan kawai tareda jan duvet ya lullu6e har kanshi dashi...kawai shidai gashi nan ne amma sam dadin jikinshi at all..wani irin weakness yakeji all over him ga kuma zuciyanshi da bai mishi dadi shima...haka nan ta kama kiranshi da sassafen Allah sai kace batada aikin yi...shi tunda yake bai ta6a ganin mayyar mace kaman Rayhan ba wlh...ace mace kaman chewing gum duk wulaqancin da yake mata har yanxu taki rabuwa dashi...haka yacigaba da juyi a kan gado shi bai koma bacci ba kuma shi bai tashi yayi abunda ya kamace shi ba...daga karshe dai da kyar ya iya mikewa yasa sport wears dinshi ya shiga jym wai ko zai dena tunanin abunda bai kamace shi ba.
Karfe uku dot yayiwa Aysha a Freedom Specialist Hospital...yau ko jiran bus bata tsaya yi ba besty ya kawota sbd tanaso ta wanke laifinta na jiya shiyasa ta fito as early as possible...tana shiga ward din taci karo da incharge na gaba daya maternity matron Salamatu sai midwife data rike mata aiki ranan da taje biki sai kuma wasu staff guda biyu da take ganinsu a eclamptic ward sai kuma alhaji Dr.Bobby dake tsaye hannayenshi zube a aljihu yana sauraronsu...wani irin dum taji gabanta ya fadi dan tasan taron bana lafia bane...Matron salamatu ceta fara ganinta dan haka tace"yauwa ga yarinyar nan doctor"..juyawa yayi a hankali ya kalleta sam baiyi mamakin ganin itace na sbd jikinshi ya bashi babu mai iya aikata wnn danyen aikin sai ita...gashi kuma hasashenshi ya zama gaskia..Aysha dai kasa tayi da kanta da sauri tana karanta lailaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimun a cikin zuciyarta...har yanxu heart beat dinta bai dawo daidai ba...saida matron ta sake yi mata mgn snn tayi karfin halin daga kafarta ta karasa ciki...daga gefe ta tsaya kanta kasa tana karanto duk abunda yazo bakinta...idanunta lumshe tasan ko bata gani ba idanunshi ke yawo a kanta dan taji wnn hadadden tsoro da firgici da take shiga idan ya kalleta...Matron ce ta fara jifanta da tambayan da ya kusa sata sakin fitsari sbd tsoro.."meya hanaki zuwa aiki jiya?.."tayi shiru tana tunanin karyar daya kamata tayi...matron ta sake cewa"kinsan asarar da kika janyo mana kuwa?..kin tafi kin bar daki ba kowa snn ga patients duk babu mai kula dasu har daya daga cikinsu ta rasu sbd carelessness dinki"...a razane ta dago tana kallon matron din abunda ta fada..she can't believe wata ta mutu sbd rashin zuwanta aiki jiya..."innalillahi wainna ilaihi rajiun mena janyoma kaina haka?.."ta fada cikin zuciyarta...lokaci guda hawaye suka ciko idonta yanxu hakan na nufin tayi kisan kai knn?...Dr.Bobby da tunda ya dora idanunshi kanta bai sauke ba ya daka mata wani tsawan daya sake firgita ta ganin yanda tayi banza da mutane kaman bada ita ake mgn ba...yace"bakida baki ne?.."da sauri ta shiga girgiza kai alamar tana dashi...ya sake tamke fuska snn yace"oya speak up..tell us exactly why u left them all alone har kika janyo mukayi asarar rai"...bakinta ta shiga motsawa tanason tace wani abu amma ta kasa...ta sai san ko kwaya takesha bazata yi karyan batada lafia ba tunda ya ganta jiya a wurin dinner... ganin batada mafita kawai ta shiga yarfa hannayenta hawaye na turereniya kan cheeks dinta tace"am...sor..ry"..Matron tace"ko dan gaba baa yin irin haka a asibiti..da kikasan bazaki zoba sai samu wata ta rike maki amma ba ki tafi ki bar patients on their own ba sbd ba wanda zaiyi tunanin su kadai ne...ba don Allah ya taimaka wadan nan sunzo jiyan ba da kilan asarar da zamuyi sai yafi haka"..kuka kawai takeyi tana gyada mata kai...Bobby ya zaro kudi a aljihu ya mikama mutum biyu da suka taimaka suka rike dakin snn yayi musu godia suka wuce...Matron da taga yanda ranshi ke 6ace tace"ayi mata uzuri dr kaga yarinya ce..zanyi mata fada inshaAllah bazata sake aikata makamancin haka ba"...bai ko kalleta ba bare tasa ran zai amsa idanunshi kan Aysha da har yanxu bata bar kuka ba yace"wuce muje"...a rikice ta dago tana kallonshi...ya zuba mata idanun nan nashi aikuwa ba shiri ta wuce gaba tana cigaba da kukanta...haka suka fito daga ward din tana gaba yana binta a baya har zuwa office dinshi...karasawa yayi seat dinshi ya zauna fuskan nan ba sarari yace"sbd bakida hankali kika wuce kika barmin patients su kadai dan bakisan aikinki ba koh?..anya kuwa bada malpractice kikayi passing Clinical skills dinki ba?.."dukda halin da take ciki mgnrshi ba karamin kular da ita yayi ba...wato ita yake nufi tana satan amsa amma Allah ya isanta wlh...cikin daga murya yace"are u deaf ina miki mgn zakimin shiru?..are u sick?.."runste idonta tayi sabbin hawaye na sake gangaro mata...itadai yau ta shiga uku da masifan wnn mutumin...sai ihu yakeyi mata kaman ita tajs ta shaqe matar ta kasheta...shima runste nashi idon yayi yana murza goshinshi trying very hard to control his temper don idan ya biye ta zuciyarshi yana iya gaggaura mata mari sbd haushin datake bashi...what did she think of herself da zai ringa mata mgn tana banza dashi...ganin bafa shiru zatayi ba ya buga table din gabanshi cikin karaji yace"kin rufemin baki ko sai na gaura maki mari a wurin...are u even alright da zaki sani a gaba kina min kuka?..are u mad?.."ya karasa mgnr cikin tsananin 6acin rai...sbd tsoratan da tayi batasan time data hadiye kukan nata tana toshe baki da hannayenta ba...shi kuma yacigaba da fadin"from today onwards aikinki ya dawo office dina...ke zaki dinga cleaning min office kullum kina wanke toilet dina...snn duk wani aike na office dina ke zaki dinga zuwa zan sallami cleaner da messenger dina har zuwa lokacin da zaki gama punishment dinki...if u like ki tafi gidan biki ku hadu da saurayinki kiqi zuwa aiki kiga yanda zanyi dake lazy fellow kawai"...har yanxun idanu a lumshe take sauraronshi...wato ma itace zata zama mishi cleaner kuma messenger sbd bashida imani...kuka kawai takeyi har yanxun batace mishi qala ba...shi kuwa kallonta yake har yanxu yana ganin yanda dimples dinta ke fitowa as a result of kukan da takeyi...ya sake daure fuska snn yace mata"go to the Nurses Station kice ina kiran Zarah"...ba tareda ta bude idon ba ta juya ta fita a office din...saida ta tsaya ta gama clearing face dinta dukda tasan a banza dan ana ganinta za'aga alamun kuka tattare da ita snn ta wuce nurses station din...tare suka fito sa nurse din zuwa office dinshi...Aysha taja gefw ta tsaya tana daure fuska dan a ganinta sbd tana mishi kuka ne yasa yake raina mata wayo...Zarah ta karasa bayan ta gaisheshi yace"how many files do we have?.."tace"they are many sir.."yace"ohk kuje da ita ki bata ta kawo and kina iya tafiya gida u are done for today"...nan da nan ta washe baki hadda risinawa tace"thank u sir"...Aysha ta maka mata wani harara a kan idon Bobby dake kallonta ta gefen ido...cikin ranta tace"azzaluma ba dole kiyi godia ba"...saura kadan daria ya subuce mishi sbd ganin yanda tayi hararan kaman idonta zasu fado kasa...tare suka sake fita Zarah ta hadata da uban files na patients din da zai gani yau snn ta koma office din nashi ta kai mishi da kyar take iya dauka sbd nauyinsu...ta ajiye mishi su nan gabanshi snn taja baya ta tsaya tareda rungume hannunta...yace"zo kiyi arranging files din according to their numbers"...sake daurw fuska tayi ta matsa ta janyo kujera zata zauna yayi saurin dakatar da ita da cewa"and who ask u to seat?.."shiru tayi tana kallonshi yace"C'mon get started before i loose my temper with u...ba dai aikinki tafia gidan biki kina barin patients su kadai ba?..as small as you are har kinsan ki hada Ap da saurayi ya sameki wani wurin sbd ba gaban parents dinki kike ba kou?..i know exactly how to deal with people like u..now start what i asked u see the other side of me"...a hankali ta matsa gaban table din ta kai hannu ta janyo files din gabanta...har zata fara dubawa ta tuna batasa glasses dinta ba dan haka ta mike zuwa inda bag dinta ke ajiye ta dauko glass din ta saka snn ta sake komawa ta fara abunda ya sata...shidai yana zaune yayi crossing hands dinshi a kirji yana kallonta...Allah ya taimaketa gaba daya files din a jere suke according to numbers dan haka ta dago tana kallonshi tace"Sir a shirye suke"...without looking at her yace"call the first person"...cikeda haushi sosai take kallonshi jin abunda yace..ta kalli bell dake gabanshi dannawa kawai fa zaiyi patients din su fara shigowa amma bazai iyaba sbd dole sai ya bata wahala...ganin wasu hawayen na sake ciko idonta ta dauki file din farko tareda juyawa ta fita sai gasu sun dawo ciki da me file din...ya nuna mata wuri ta zauna ita kuma Aysha ta kwashi files din gaba daya zata fita dasu yace"where do u think u are going?.."ba tareda ta juyo ba tace"waje.."yace"su kuma files din suyi mene a wajen?..and ke kanki waya baki permission din zuwa waje?.."saida ta hadiye tears dinta snn tayi qundunbala ta juya tana kallon tsakiyar idonshi trying so hard ta 6oye tsoronshi dake cikin nata idanun tace"sai nacigaba da turosu daga waje"...kallon tsakiyar nata idanun shima yayi kafin yace"zo ki ajiyemin files and if u dare step out of this office sai na baki mamaki wlh"...sauke idonta qasa tayi tareda lumshe su allowing tears dake ciki fitowa kan cheeks dinta...ai ita tasan ta gama yawo tunda ta fada hannun wnn azzalumin...bata damu data goge hawayen ba ta maida mishi files din gabanshi kaman yanda yace snn ta koma gefe ta tsaya tana cigaba da hawaye...hankalinshi ya maida kan patient dinshi yana mata tambayoyi...Aysha tayi mamaki sosai yanda taga yana interacting da patients din nashi sam batayi zaton haka daga wurinshi ba...gani take ko patients din ma zare musu ido zai ringayi yana daure musu fuska amma sai taga ba hake yakeyi ba sam...mgn yakeyi dasu full of attention da kuma concern kamar dai ba arrogant and wicked Proprietor dinsu ba...haka yacigaba da attending patients dinshi tana tsaye saidai idan ya gama yace ta kira next patient and ba yanda ta iya haka tayita sintiri from office dinshi zuwa waje...legs dinta har sun fara mata ciwo sbd tsaiwa ga wnn kai kawon da takeyi shima ba karamin wahala ne dashi ba...ga patients din da masifan yawa dan gani take kaman ma karosu akeyi ace tun dazu suna abu daya amma har yanxun sunki karewa...har aka kira sallahn magrib basu kammala ba...zuwa yanxun karfinta ya gama karewa tass neman wanda zata saukema kukan dake cinta kawai takeyi amma babu dan haka ta jingina da bango tareda kai hands dinta ta rufe fuskanta dasu ta shiga rera kukanta a hankali...Bobby na jinta baice komai ba har ya sallami wadda take gabanshi snn ya mike zuwa bathroom yayo alwala ya fito ko kallon inda take baiyi ba ya fice zuwa masjid...tana jin ya fita ta zauna nan kasa zaman dirshan ta dora hannu a kanta tana rushewa da wani matsanancin kuka...kuka take sosai dan idan ka ganta zaka ranste da Allah wani gagarumin abun akayi mata...saida ta shafe kusan minti goma tana abu daya kafin ta mike da sauri kaman wanda ta tuno wani abu ta dauki bag dinta tana goge hawayenta ta bude office din ta fita...a bakin kofa sukayi karo dashi yana tsaye ya zuba mata ido kaman yasan abunda take niyyar yi yace mata"waya baki permission din tafiya?.."takai hannu ta goge tears dinta ta bude baki da kyar sbd kukan da taci tace"Sir...dan..Allah...inje gida...wlh na gaji...kaina namin ciwo"...kallonta kawai yake yanda tayi mgn dama tun ba yanxu ba yasan sangartacciya ce so baiyi mamaki ba sam...baice komai ba yakai hannu ya bude kofar office din yana binta wnn kallon da bataso cikin stern voice dinshi yace"get in.."yarfe hannu ta farayi tana dan bubbuga legs dinta a kasa da alama abun ya motsa cikin shehssheka tace"Sir dan...Muhammdu...Rasulillahi...dan darajan..."kasa karasawa tayi sbd ido daya tsareta dasu...haka nan ta juya ta koma office din sabbin hawaye na sake antayowa fuskanta...shima shiya yayi ya maida kofan ya rufe snn ya karasa seat dinshi ya zauna...ya duba sauran files da suka rage mishi yaga guda uku yasan idan yace ta kirasu 6ata mishi time zatayi dan haka ya danna kararrawa ba dadewa wanda yake kan layi ya shigo...wuri ya nuna mata ta zauna snn ya shiga attending dinta...Aysha dai har yanxun tana tsaye tana kuka kaman wanda akama dan banzan duka...ganin bafa dena kukan zatayi ba daya sallami ta gabanshi sai ya juya yana watsa mata harara yace"ke kinada hankali kuwa?..office din nawa zaki maida wurin iskancinki are u insane?.."banza tayi dashi tana cigaba da kukanta...ya daka mata tsawa yace"are u deaf"...ai batasan lokacin data hadiye ragowar kukan ba sbd tsabar tsoratan da tayi...ya nuna mata wani seat dake kusada ita yace"seat down and keep shut...idan kika sake na sake miki mgn you will see the other side of me"...ba musu ta zauna kan kujeran tana kunshe kukanta...haka tayita zaune har ya karasa ganin patients din snn ya mike ya tattara kayanshi ya dau keys da wayoyinshi ba tareda ya kalleta ba yace"leave my office immediately..and make sure gobe ki fito da wuri kimin clearing office idan ba hakaba zakiga yanda zanyi dake"...tun kafin ya karasa ta bude office din ta fita da sauri tana sakin kukan da take rike dashi tun daxu.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
18
Parking lot ta zauna tacigaba da rusa kuka kaman wadda aka aikoma saqon mutuwa...tana nan zaune taga fitar motanshi aikam tabi motan da harara kamar idanun zasu fadi...saida tayi me isarta snn ta daga waya ta kira besty dan yazo yayi picking dinta...yana dauka ko mgn kasawa tayi kawai ta rushe mishi da kuka...a rikice sosai Sa'eed ke tambayan abunda ya sameta amma ko uffan batace ba sai azabar kuka take...daga karshe sai ya kashe wayan kawai snn ya dauki hanyan Hospital dama he is near by so within few minutes ya iso...da sauri ya karasa inda ya hangota zaune tana kuka shima ya zauna nan gefenta hankalinshi duk a tashe yace"besty dan Allah what is it?..why are u crying like this?..are u sick?.."girgiza mishi kai tayi meaning she is fine...yace"then what happened?..why are u crying?.."kuka tacigaba dayi kaman bazata yi mgn ba sai can daga baya tayi kokari ta tsayar da kukan nata snn tayi mishi bayanin duk abunda ya faru tun shigowarta asibitin zuwa yanxu...sauraronta yake saida ta gama tsaf snn yace mata"yanxu dai kiyi hakuri ki fara mikewa mu wuce kinga dare na karayi sosai...shi kuma proprietor kiyi mishi addu'a Allah zai saka maki kinji kou?.."gyada kanta tayi tareda mikewa a hankali suka nufi inda yayi parking...if u see how she is walking u will think irin tayi shekara da shekaru tana ciwon kafa...a haka suka isa inda motan yake ya bude mata ta shiga shima ya shiga suka fita daga asibitin...koda suka isa hostel saida ya kira Billy a waya wai tazo ta shiga da ita ciki aikuwa ta fito a rikice dan tana tunanin wani mugun abun ne ya faru da ita...mamaki ya kamata ganin yanda idon 'yar uwar tata yayi ja sosai face dinta duk yayi red sbd kukan dataci kafin ma ta tambaya Sa'eed ya labarta mata abunda Ayshan ta fada mashi ya faru...jikinta yayi sanyi kalau ita kanta tausayin Ayshan takeji...tasan haduwa irin wnn da proprietor ba abun alkhairi bane mutumin da ko idanu ka hada dashi sai kaji a jikinka inaga kuma ace ya tsareka da a gaba yana suburbuda maka masifa...ai dole ma Aysha ta jigata wlh..ko ba don zirga zirgan da tayi ba ko zama at the same roof da wnn mutumin kadai ya isa yasa mata zazza6i balle kuma ga wahalar da ita da yayi...Allah kadai yasan adadin sau nawa cikinta na kadawa sbd wmn matsiyacin kallon nashi...a hankali ta kamata suka shiga hostel din shi kuma Sa'eed ya juya kan motarshi ya wuce gida...suna shiga ciki ta hada mata warm water ta taimaka mata zuwa bathroom snn ta dawo ta shiga kitchen ta hado mata thick tea shima mai zafi ta jiye mata kan study table...ta dauko pcm da ruwa shima ta ajiye mata nan kusada tean sai kuma ta bude wardrobe dinta ta dauko mata jessy dinta as usual na Man Utd fara qal da wandonta duk ta jiye mata su kan gado...tana fitowa ta dauki kayan ta saka snn tasha tea da magani snn ta nannade kan gado tana sauke ajiyar zuciya...kawai imagining take yanda zatayi spending three whole weeks tareda wnn azzalumin mutumin da baida imani da tausayi ko kadan.
Washegari da wuri ta tashi duk da ba wani baccin kirki ta samu ba amma she woke up as early as possible sbd gudun sake yin wani laifin...a gurguje ta shiga bathroom tayi wanka snn tazo ta shirya suka fita tareda Billy ko breakfast ta kasa tsayawa tayi sbd tsoron kar tayi latti ya samu daman ci mata mutunchi.
8:17 suka shigo Hospital ko sallaman kirki bata tsaya sunyi da Billy ba ta wuce sbd tsoron abunda zai iya mata...saida ta tsaya ta gama jero addu'o'inta a bakin office dinshi snn ta tura kofan ta shiga a hankali da sallamanta ciki ciki...yana zaune kan office chair dinshi sanye da suit as always yana filling wani file dake kan table dinshi...ko kallon inda take baiyi ba balle har tasa ran zai amsa sallaman da tayi..itama hakan bai dameta ba ta karasa inda ta tsaya jiya ta tsaya kanta a kasa...wayanshi ne keta ringing yana ciki file din amma yayi banza dashi kaman bashi ake kira ba...saida ya gama snn yayi sliding tareda putting nata on speaker da igbo yace"Sab bakada hankali kou?..why kaketa jeramin missed calls haka?.."daga daya bangaren Sab ya amsa mishi cikin igbo shima saying yanason mgn dashi ne...Aysha dai na tsaye tana jin yanda suke mgn da igbo dagashi har wanda ya kirashi a wayan...dukda ba fahimtan language din takeba for sure tasan masifa yake sbd yanda yake daga murya...can kasa kasa tace"duk wani inyamuri dai ya iya masifa..kilan abun a jininsu yake"...tayi nisa cikin tunaninda take har batasan ya kammalan wayan da yake ya dawo sa hankalinshi gareta ba...yana kallon yanda dan bakinta ke motsawa as a result of zancen zuci da take kawai sai yaji gabanshi ya fadi...ya lumshe ido yana karanta innalillahi cikin ranshi...ya dauki tsahon lokaci idon nashi a rufe har saida yaji heartbeat dinshi ya daidaita snn ya bude..still kuma idanun kanta suka fada this time around sai ya kasa dauke idanun daga kanta...he just keep staring at her like mirror...har yanxun bakinta mosti yake and he wonder what she's saying da bakin ke motsawa haka...a hankali yayi sama da eyes dinshi zuwa forehead dinta da black thick hair kenan a kwance luf kaman na jaririya har zuwa sajenta da kuma dimples dinta da ko yaya cheeks dinta yayi motsi sai ya fito...sake lumshe eyes dinshi yayi yana dan murza goshinshi feeling somehow...baisan meya sameshi yau ya kasa dena kallonta ba and it's not as if she's beautiful kawai dai baisan dalili ba...wnn karon yana bude idon itama ta bude nata aikuwa idanunsu suka sarke cikin juna...Aysha da dauke nata da sauri sbd wnn abun dai da takeji duk ya zuba mata golden eyes dinshi a kanta...turo baki tayi murya can kasa tace"nidai Allah ya isana wlh..haka nan ya dinga zubama mutane idanun nan nashi sbd yasan ba'aso"...daure fuska yayi kafin yace"ke what are u saying?.."da sauri ta maida bakinta normal tareda kokarin daidaita face dinta kai a kasa tace"ba komai Sir...good morning"...bai amsa ba sai nuna forehead dinta da yayi yace"baki iya daura dankwali bane?..ko duk cikin rashin sanin darajar kai ne yasa kike yawo da gashi a waje?.."hannu takai ta dan janyo hijab din zuwa goshinta dukda ba rufe gashin yake ba dan kome zatasa sai ya fito shiyasa ma take barinshi..cikin ranta tace"na rasa a ina inyamurin nan yaji hausa wlh..he speaks like jakin kano"...kallon forehead din nata yayi yaga still gashin na nan waje kuma wai da sunan ta rufe kawai sai ya girgiza kai tareda sakin tsaki...mikewa yayi ya dauki phone dinshi snn ya kama hanyan fita yace mata"follow me"...ba musu tabishi a baya kaman body guard...eclmaptic ward taga ya nufa...ya jima suna mgn da wata nurse da doctors guda biyu kan wata patient da zasu shiga da ita theathre yanxu...after like ten minutes aka fito da matar zuwa theatre sauran doctors din suma duk suka shiga don shiryawa...shine karshen fitowa shima ya kama hanyan theatrn Aysha ta bishi a baya...daga bakin kofa ta tsaya ta dan daga murya yanda zai jiyota tace"Sir in koma knn?.."juyowa yayi yana kallonta da mamaki yace"go back where?..ba cewa nayi ki biyoni ba"...ta dan marairaice tace"to Sir naga zaku shiga theatre nefa"...ya daure fuska snn yace"C'mon come inside and get ready dake zamu shiga ai"...ta wani zarw idanu tana kallonshi hadda dora hannu a chest dinta tace"dani kuma?.."yace"ke don't waste my time here.. i said dake zamu shiga kiyi resuscitating baby and don't let me repeat myself"...hannu ta fara yarfewa zata kwaso magiya kawai ya zuba mata idanunshi yana yi mata irin kallon da yasan duk iskancinta bata isa ta sake yi masa musu ba...hakan ne kuwa ya faru dan kasa cewa uffan tayi..tayi kasa da kai cikin ranta tana mamakin tasirin da eyes dinshi suke dashi a kanta...kofa ya nuna mata yana kallonta alaman she should enter...ba musu balle gardama ta shigo ciki a hankali kaman mara lafia...changing room ya nuna mata ba tareda yace komai ba haka ta shiga ciki tanajin kaman ta dora hannu a kai tace wayyo Allah...bayan ta shiga shima ya shiga doctors changing room yayi changing zuwa theater outfit dinsu snn ya fito zuwa main theatre...matar tana kwance masu anaesthesia sun fara aikinsu a kanta sai doctor faith da doc gabriel da zasuyi aikin tare...ganin har zasu fara bata fito ba ya fita zuwa dressing room din...a tsaye ya sameta ta gama sa kayan sai kallon kanta take tana ganin yanda kayan sukayi mata yawa...tana turo baki tace"kayan ma over size n..."bata karasa idanunta ya sauka cikin nashi sai tayi saurin daidaita kanta da sauri tana cewa"am sir..d..dama yanxun..zan fito"...kallonta yayi from head to toe snn ya tsayar da idon nashi kan gashinta datayi parking a tsakiyar kai ta saki jelar yanata yawo tsakanin wuya da shoulders dinta...da sauri ta dauki hijab dinta ta rufe kan nata dashi baki a tunzure tana fadin"to babu hula fa"...baice mata komai ba ya karasa cikin dakin ya bude wani drawer ya zaro mata one of huluna da suke ciki snn ya wurga mata...saida ta daure fuskanta tsaf snn ta dau hulan ta saka cikin ranta tana zaginshi sbd cilla mata hulan da yayi...hanya ya nuna mata ba musu ta shige gaba yabita a baya...a bakin main theater suka tsaya ta zura wnn gunduma gunduman takalman snn suka shiga ciki...itadai a tsorace take dan bata ta6a shiga theatre ba..tsananin tsoronta ma bazai bari ta shigaba dan ko Allah ya san batason ganin ana yanka mutum sam...amma yau wnn inyamurin ya sanyata dole ta shiga dukda rashin son nata...saida suka gama shirya komai tsaf snn kowa yasa nose mask dinshi suka fara aikinsu...Aysha dai na tsaye tana faman runste ido don bazata iya gani ba wlh...Bobby dayaga yanda take runtse ido sai yayi mata alama da ta matso kusa...ta shiga yarfa hannu har ta fara hawaye shi kuma ya tsareta da ido yanda baza tayi mishi gardama ba...haka ta matsa inda ya nuna mata tana cigaba da hawaye har doc Gabriel nayi mata daria...kafin ta sake kulle idon yace mata"if u dare close those eyes again zakiga yanda zanyi dake wlh..and i mean it"...bata rufe din ba kuwa ta zuba idanu kawai tana kallon abunda sukeyi...kirjinta har sama da kasa yakeyi bata ta6a sanin tanada tsoro har haka ba sai yanxu...hankalinta bai sake tashi ba saida taga sun fara yanka matar...taga yanda suke cutting skin dinta layer by layer kawai sai taji wani hadadden jiri ya fara daukanta...kokari tayi ta rike gefen gadon gam still kuma taki kulle idon sbd kar yayi mata masifa...tun tana iya bakin kokarinta wajen ganin jirin baiyi tasiri a kanta ba har yakai limit din da bazata iya controlling dinshi ba kawai sai gani tayi dakin yana juyawa da ita...ta saki gadon da sauri tareda kai hannu ta dafe head dinta dashi idanunta a rufe still bata dena ganin jirin ba daga karshe ma sai ji tayi ta tafi luuu kaman zata fadi Allah ya taimaka akwai wani gado a bayanta kawai saita fada kanshi ji kake timm...a tare gaba daya doctors din suka dago suna kallonta don sunyi nisa a aikinsu that ba wanda ya lura da abunda ke faruwa da ita sai faduwan nata sukaji...dukda ta fadin kuma jirin bai dena daukanta ba har yanxun tana dafe da kanta hawaye na fitowa idanunta murya can kasa take fadin"wayyo Ammina..wayyo dadyna..wayyo Allahna"...gaba daya doctors din saida sukayi daria banda Bobby da baiga anything funny a nan ba...basubi ta kanta ba suka cigaba da aikinsu that last for 40 to 45 mins kafin suka gama...doc faith ce tayi resuscitating baby su kuma suka karasa duk wani necessary abu da zaa yima matar snn wanda zasu fita da ita sukazo suka dorata kan trolley sukayi waje da ita babynta kuma already an mikashi wa relatives dinta...sauran doctors din suma duk fita sukayi shi kuma Bobby bayan yayi sanitizing hannunshi ya nufi kan gadon da take thinking ko bacci take mishi a theatre and to his biggest surprise sai yaga ashe sumewa tayi...mamaki ne ya kamashi hade da daria at the same time...wato duk iskancin dan iska akwai abunda yake tsorata shi har ya sashi suman dole...shi tunda yake bai ta6a ganin Midwife irinta ba...wai matar dake dealing da kar6an haihuwa itace zata suma sbd Caesarean section "what a shame!.."ya fada trying to control his laugher cox he still can't believe sumewa tayi...wato duk rashin jin nan nata she has this phobia of blood ne ko of the operation din ne gaba daya ma bai sani ba...saida ya gama dariyarshi snn yasa aka kawo ruwa ya watsa mata...ta mike a gigice idanunta kulle take fadin" dan Allah no...i don't want to see it plss i beg u...wayyo Allah besty,Billy,baby come help me plssss"...ta karasa mgn new tears na rolling kan fuskanta...Dr.Bobby still can't believe this...knn da gaske suma tayi sbd abunda ta gani...lallai kuwa tanada aiki a gabanta...a very huge one ma kuwa...a hankali ta bude idonta sai taci karo da smiling face dinshi aikuwa ta wara idanun da kyau tana kallonshi to make sure she is not dreaming...tadai san idan ba mafarki ba ba yanda za'ayi inyamurin nan yayi daria for it's something she never seen..shi kuma ganin kallon da take masa sai ya dinke fuskanshi tsaf tareda matsawa daga inda yake yace"C'mon get dawn before i slap u lazy girl kawai...a haka zaki zama midwife kina painting sbd caesarean?..u are deceiving ur self"...goge tears dinta tayi ta sauko daga gadon tana fadin"ai ni ba ta6a gani bane shiyasa"...harara ya watsa mata yace"shiyasa nace u are deceiving ur self...now ki wuce ki jirani office and if u like kije wani wurin kiga idan na dawo banyi maganinki ba"...wucewa tayi tana sake turo baki sai kuma ta juyo zatayi mishi mgn yace"i said leave"...ba gardama ta sake juyawa ta fice daga wurin...duk jikinta ma wani iri take jinshi kaman na mara lafia...shiko Bobby bayan yayi changing zuwa normal outfit dinshi ya fita zuwa office...zaune ya sameta kan one of sofas dake nan ciki tayi wani dai dai kaman tana office dinta yana shigowa ta mike da sauri tana rarraba ido kamar munafuka...baice mata komai ba ya karasa gaban table dinshi ya dauki stethoscope ya rataya a wuya snn ya juya zai fita ya sake ce mata"Follow me"...banza tayi dashi tana binshi da harara har ya fita snn ta mike itama ta fita tana kwaikwayon mgnrshi" wani wai follow me...sai kace ajiyeni yayi in dinga yi masa bauta...mugu kawai"...ta karasa mgnr da guntun hawaye a idonta...ita dai zataga ranar da zatazo asibitin nan ta tafi bai sa tayi kuka ba...kullum burinshi ya sata yin abunda bataso ko ya wahalar da ita kawai sbd small mistake data aikata bayan ba kanta aka fara ba...Post natal ward suka je ya fara ward round ita kuma tana biye dashi a baya...data gaji da tsaiwa sai ta faki idonshi ta samu wuri zata zauna taji yace mata"zo kimin taking vital signs din wnn"...kamar ta kwada masa mari haka taji amma ba yanda ta iya haka ta mike ta fara taking vital signs din...a takaice ita ta dauki vital signs din duk patients din dake ward din shi kuma yana dubasu...kafin su gama kuwa jikinta yayi laushi liss kaman an nakada mata shegen duka...yau ma kamar jiya da kuka ta fita daga office dinshi bayan ya sallameta.
Haka kwanaki sukayita tafiya kullum Aysha na shan baqar wahala a wajenshi dan ba ranan da zatazo ta wuce bai sata kuka ba...gashi ita kuma ta kasa sabawa da wahalar da yake bata kullum idan ta gani bata ma sanin yaushe kukan ke zuwa...a haka suka kwashe two weeks suna abu daya har suka shiga sati na uku wich is their final week daga shi zakuyi resuming school...if u see how she is happy zakayi zaton graduation ne zatayi gaba daya...nan kuwa murna take sbd Allah ya kawo karshen wahalar da takesha hannunshi dan ko makiyinta bazata yi mishi fatan ya shiga hannun dr bobby ba dan bashda kyau ko kadan...cikakken mara mutunchi ne na gidan gaba shiyasa take addu'a idam sun rabu a nan Allah yasa rabuwarsu knn dan ko a College bata fatan ko hanya su sake hadawa dashi...laf cikinsu ita kadai ce batayi rotating wards ba sbd yanda ya makaleta a office dinshi amma su sauran kusan wards uku kowacce taje...ita Billy daga ANC ta koma Family Planning Unit daga nan kuma taje Ante Natal Ward duk tayi two two weeks a wurin amma ita duk yabi ya takureta a wuri daya ya hanata gaba ya hanata baya sbd baqin hali irin nashi...ita har yanxu tana mamaki idan akace mata musulmi ne dan har ga Allah wnn baqin halin nashi ba idabi'an musulman kwarai bane..ko da yake shima kilan musulmin ne kawai amma bana kwarai ba...shiyasa dole ma tayi murna Allah zai rabata dashi ta huta da ja'iba.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitar min dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
19
Yau Thursday Aysha na zaune office dinshi ita kadai as shi tunda ya fita sallah bai dawoba dan haka ta bararraje abunta tana ta faman waya da Babynta da har yanxun bai dawo daga tafiyar da yayi ba...bayan sun kammala wayan tayi dialing number Ammi dan da gaske so take taje gida weekend amma Hamma yace wai ta bari ba yanxu ba...ringing biyu Husna ta daga wayan tana cewa"Addah.."tace"na'am ina Ammi?.."Husna ta dan turo baki tace"ke Adda bakida kirki wlh..daga daga wayan zaki wani ce ina Ammi ko gaisawa bazaki bari muyi ba?.."dan murmushi ta saki tana gyara zamanta tace"to sannu Husna ina yini..ya gida ya studies?.."daria Husna tasa jin yanda take gaisheta tace"kai Addah"...itama tana cigaba da smiling tace"to ai naga ba'a iya maki ne shiyasa na gaisheki"...Husna tace"umh to ina nan lafia ya posting?.."da sauri kaman wadda aka tsikara tace"posting dai yazo karshe ki tayani murna wlh..gobe Allah zai rabani da inyamuri in huta da azaba"...daria Husna ta sakeyi tace"nifa Adda har yanxu daria kike bani idan kika kirashi inyamuri..ina laifin ma kice dr bobby"...ta6e baki Aysha tayi tace"ki zauna saina kirashi dr bobby...mutuminda kowa yasan inyamuri ne shi..ranar bakiji wayan da naji yanayi da wani ba kilan dan uwanshi ne sukata inyamurancinsu abunsu"...sauke ajiyar zuciya Husna tayi tace"to congratulations Allah zai rabaki dashi gobe..amma zaku iya haduwa a cikin college fa"...tun kafin ta rufe baki Aysha tace"bakinki ya sari danyen kashi..nidai kiba Ammi waya inyi mgn da ita..where is my habibty?.."tace"yanxun nan suka fita da Hamma...Ammi kuma tana daki tace bacci zatayi kar in tasheta"...Aysha tace"karya kikeyi dan Allah ki kai mata it's urgent plss pls plss..kinji 'yar kanwata"...kafin Husna tayi mgn ta jiyo voice din Ammi tana cewa"Husna daukan min waya kikay kou?.."da sauri ta mika mata wayan tace"dama Adda ce ta kira gashi"...batayi mgn ba tasa hannu ta amsa wayan...Aysha ta wani narke kamar tana gaban Ammin tace"my Ammi"..tsaki Ammi taja tace"zakiyi mgn ko bazakiyi ba?.."ta sake narkewa tace"Ammi zanyi...amma fa nayi missing dinki sosai wlh...wai yanxu Ammi ni ko dan pampering dina sbd bana gida bazakiyi ba kuma fa nice fisrt love dinki tunda ni kika fara haif..."bata karasa ba Ammi tace"Aysha zakici ubanki wlh...abokiyar wasanki ne ni da zakina fadamin such maganganu..wato sbd kinga kwana biyu kinata zuba rashin mutuncinka na kyaleki kou?..to zaki dawo gidan nan ki sameni zany maganinki"...da sauri tace"Ammi am sorry dan Allah...kiyi hakuri ban karawa"...wani tsaki Ammi ta kuma ja tace"naji...yanxun zaki fadi ur reason for calling ko kuma iskancin naki zaki cigaba dayi?.."ta wani marairaice kaman abun tausayi tace"zan fada...Ammi dama fa so nake nazo gida weekend shine hamma wai ba yanxu ba...dan Allah Ammi kice yazo ya daukoni kinji..wlh ina missing dinku"...kai tsaye Ammi tace"saidai kuwa kiyi hakuri dan gobe muma zamu wuce Abuja nasan shiyasa yace ki hakura..amma idan muka dawo ai zakizo so stop worrying urself"...da sauri tace"Ammi me zakuyi a Abuja kuma?.."tace"wani taro ne nasu daddynku akayi inviting dinmu and daga ni sai Najeeb zamu tafi banda su Husna dan nasan yanxun xaki ce an tafi dasu baa tafi dake ba...nasan sbd irin wnn halin naki dadyn ma yace a kyalesu a gida"...ba kunya har wani ajiyar zuciya ta sauke dan wlh da zaaje dasu itama daga hankali zatayi sai an biyo an tafi da ita...yanxu kuwa da taji babu su sai taji hankalinta ya kwanta..zuwa weekend dinma ta hakura idan suka dawo din sai taje...a hankali tace"to shikenan Ammi sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya"...Ammi ta amsa da"Ameen"snn sukayi sallama...tana ajiye wayan idonta ya sauka kan Bobby dake zaune yayi relaxing kan seat dinshi yana kallonta...ta zare idanu sosai hade da dora hannu a kirji cikin tsananin tsoron ko yaji abubuwanda ta fada a kanshi tace"Na shiga uku"...saura kiris daria ya su6uce mishi amma ya fuske...instead sai ya daure fuskanshi yace"so abunda kikeyi min a office knn idan bana nan kou?..yayi miki kyau"...hadiye wani yawu tayi da kyar cikin karfin hali tace"Sir..dan Allah am sorry...kaji"...ko kallonta baiyi ba ya mika mata hannunshi yace"bani wayan"..a razane tace"wich one?.."yace"ur phone"...nan take ta sake tsurewa duk a tunaninta yaji gulmanshi da sukayi tace"Sir dan darajan su Mummy kayi hakuri"...kallonta kawai yayi hade da girgiza kai yacigaba da aikinshi bai sake cewa komai ba...ita kuwa daukan wayan tayi ta turashi cikin jaka tana addu'an Allah yasa baiji wayan da sukayi da Husna ba...karfe uku ya sallameta as usual tana fitowa suka hadu da Billy da sauran 'yan hostel suka karasa inda bus dinsu yake duk suka shiga sai Hostel dinsu.
The following day duk da wuri suka shigo sbd friday gajeren rana ce and kowa tanaso a sallameta da wuri sbd su samu su wuce...lokacinda ta isa office dinshi yanata attending patients sai ta nemi wuri ta zauna kamar yanda ta saba tana sauraron discussion dinsu..wasa wasa tayi learning abubuwa da dama zaman da tayi office dinshi don sata gaba yake idan yana interacting da patient yace idan sun gama zaiyi mata tambayoyi dan haka take bude brain dinta da kyau tana kwashe duk abunda yake fadi..haka duk prescription din da yayi saiya nuna mata nan ma idan sun gama ya shiga mata tambayoyi iri iri so he've learned alot and ko ba komai ta wnn fannin dai zatace yayi abun kirki...da yake patients din ba masu yawa bane around 12 ya gama dasu snn ya fara shirin tafia sallahn jumu'a...before ya fita ya bata log book dinta da yayi signing already snn ya nuna mata kofa yace"A sauka lafia"...wani kayataccen smile ta saki da har both dimples dinta suka bayyana cikin tsantsan farin cikin zata rabu dashi tace"nagode sir"..daga haka ta fice daga office din bobby ya bita da kallo irin na mamaki...tunda yake da ita bai ta6a ganin such smile kan face dinta ba...yanxun duk wnn excitement daya gani kan face dinta na rabuwa dashi ne ko kuwa there is more to it?..kai ai daga gani ma wnn na rabuwa dashi ne...haka nan kuma sai yaji baiji dadin yanda tayi ba.."am i this bad?.."ya fada a fili kaman he's asking someone...ganin yana wasting time dinshi a banza kawai ya fita zuwa parking lot driver na ganoshi ya bude mishi mota ya shiga suka fita daga asibitin.
Ita kuwa Aysha office din da aka fara posting dinsu taje nan ta samu sauran colleagues dinta a wurin kowacce an sallameta an kuma yi mata signing... daga nan aka basu certificate shknn aka sallamesu kowa ta kama gabanta...ita da Billy tare suka fito zuwa parking lot amma basuga motan Sa'eed da yace zaizo daukansu ba...suna kokarin zama sai gashi nan ya karaso dan haka suka karasa inda yayi parking...ko a hanya Aysha kasa 6oye excitement dinta tayi Billy sai tsokanarta take wai daga yanxu tanayi mata laifi zata hadata da proprietor tunda shine maganinta...ita kuwa sai hakilo take bestynta na tayata...yana ajiyesu a hostel suka shiga ciki shima ya wuce.
Around 5 pm suna zaune room 3a gaba daya sai labari suke suke darawa...they are all happy sun gama Clinical Posting dinsu lafia...wayan Aysha data bari cikin dakinsu nata ringing bata ji ba sbd hayaniyan da sukeyi...wata da tazo wucewa taji ringing din shine ta dauka ta kai mata dakin da suke...tana duba screen taga Baby boo jiki sai ta mike da sauri ta fita daga dakin tana fadin"my husband is calling"...Rahma tabita da kallo tana daria tace"Billy wai ina mgnr Sir Abdool ya kwana ne naga Lamido har tayi mishi kishiya sbd wulakanci"...Billy tace"ki bari kawai wlh tunda nake ban ta6a ganin mace kaman Lamido ba...she is indirectly rejecting him for that sugar daddy"...gaba daya daria suka saka kafin wata tace"nima dai ina mamakinta wlh..ta samu mutum kmr sir abdool da yake bala'in sonta wai ta kyaleshi for someone else..she is kind of different"...nan kuma akalar hiran nasu ya koma kan Lamido and her love for sugar daddies kowa yana fadan albarkacin bakinshi...tana fita ta fada room dinsu hadda rufe kofa snn tayi picking...before she says anything yace"My baby am back"...wani ihu data saka saida ya janye wayan daga kunnenshi...lokaci daya kuma ta toshe bakinta tana zaro ido feeling so ashamed of herself for behaving like this...sam batasan sanda ihun yayi escaping bakinta ba wlh..she is just super excited he's back dama ga farin ciki rabuwa da inyamuri ga kuma another good news...shi kuwa Prof daria ya saki sosai jin tayi diff kaman ruwa ya cinyeta yace"baby girl why are u quite?."kamae zatasa kuka tace"sorry...ban san yaushe ya fito ba wlh..am just happy u are back"...murmushi ya kara saki yace" don't worry yanxun dai ki samu ki fito waje in ganki"...idanu ta sake budewa tace"wait..u mean kana hostel dinmu?.."yace"komai bazan iya yi ba har sai na ganki"...ai bata jira ya karasa ba ta kashe wayan da sauri ta rarumi hijab din Billy dake nan kan bed dinta ta dora kan jean da shirt dake jikinta ta zura takalma ta fita...a bakin gate din nasu kuwa ta ga motanshi batasan time data saki murmushi tana karasawa wurin ba...bude mata motan yayi ta shiga snn ta rufe ta juya tana kallonshi...kallon nata shima yakeyi yanajin tamkar bai ta6a missing wata halitta ba kaman yanda yayi missing dinta...ita kuwa banda murmushi ba abunda takeyi...a hankali taji ya kira sunanta"Ayshaa.."ta sake dagowa tana kallonshi don tunda suke bata ta6a jin ya kirata da Aysha ba...before she says anything yayi adding"Baby girl am tired plss...am tired of this hide and seek i really want to meet ur dad..i need to talk to him about us..about our marriage am not a small boy da zanyita wasting time dina ina soyayya a waje"...shiru tayi tana sauraronshi thinking of what to tell him...har ga Allah ba wai batason aurenshi bane no kawai dai tafiso ta fara kammala karatunta then sai ayi mgnr aure amma ta fuskanci he won't let that happen...his last statement yasa ta dan kwa6e fuskanta kaman zata fashe da kuka tace"wato wasting time dinka kakeyi ma kou?..soyayya dani shine waste of tim..."bata karasa na ya katseta da fadin"No baby that's not what i mean...ina nufin am tired..i want to marry you plss"...batasan time din da ta saki murmushi sbd yanda yayi da face dinshi ba...tana dubanshi tace"baby saurin me kakeyi ne?..xaka aureni inshaAllah.."zai sake mgn tace"Please mana..k ganinka ban gamayi ba ka fara wani mgn daban..nidai allow me to look at u sosai inyaso daga baya sai muyi mgnr auren"...murmushi ya saki yana girgiza kanshi sarai ya ganeta..wai shi yarinyar nan zatayi ma wayo...bai sake cewa komai din ba kuwa sukaita kallon junansu kaman wanda suke staring competition...har tafiya ta hanashi wai bata gaji da kallonshi ba...haka yayita zaune har sai da aka fara kiran magrib snn ta kyaleshi ya tafi ita kuma ta koma hostel.
Washegari saturday Bobby tunda ya gama gyming dinshi yayi wanka ya fito suke zaune parlor tareda Mummy da aunty sumy sai labari suke...Nur ne ya shigo parlon da sallama Bobby ya wani hade rai yana kallonshi...yasan tunda yazo gidan nan fita yakeso suyi shi kuma baida intention na zuwa ko ina yau...he wanted to stay home yayi enjoying weekend dinshi like any other person amma it’s like Nur yana baqin ciki da haka...har ya iso cikin parlon ya zauna baice mishi qala ba yanaji suna gaisawa da mummy da aunty sumy sai yayi kaman bai jinsu ya shiga danna wayarshi...bayan sun gama gaisawa Nur ya daga kanshi yana kallon Bobby yaga yanda ya hade giran sama dana qasa kawai sai ya dan girgiza kai yana murmushi...yasan duk wnn attitude da ya fara displaying sbd baison fita ne and shi kuma ya ranste yau din nan sai ya fita dashi sai suga yanda za’ayi...hankalinshi ya mayar kan mummy ya wani tattara gaba daya nutsuwa da kamun kanshi yace"mummy alfarma nazo nema a wajenki dama"...mummy tace"to ina sauraronka Nuru"...yace"ai kinsan ana gina new apartments a college hostel koh?.."Mummy ta gyada kai alaman ta sani...yace"to wlh mummy tun last week mukayi mgn da engineer nan yace ya kamata muje da akwai abunda zai nuna mana amma bobby sam yaki zuwa...yanxun ma da kika ganni kirana yayi yace yana can site din yanaso mu hadu sbd gobe zaiyi tafia kuma zai iya daukan lokaci bai dawoba shiyasa na fito..nasan kona fada masa ba yadda zaiyi ba shiyasa nace gara in biyo ta wajenki"...murmushi kawai mummy tayi tana kallonshi kafin ta juya tana kallon Bobby da har yanxun ran nan a hade yana 6a66ata rai...daria ta saki sosai tana kallonsu...wnn draman nasu ba yanxu aka fara ba...shi Bobby nada taurin kai da kafiya shi kuma Nur akwai naci shiyasa duk irin haka ya hadasu kai tsaye yake zuwa wurinta dan yasan itace kadai zata iya sanyashi ya aikata abu ko bayaso...aunty sumy ma dake zaune tana kallonsu daria take...mummy ta sake juyawa tana duban Bobby tace"ai kaji me abokinka ya fada kou?.."da sauri yace"mummy don’t mind him dan Allah makaryaci ne kawai...babban burinshi yaga ya fitar dani daga gida kuma yasan bai isaba shine zai biyo ta hannunki"...juyawa ta sakeyi tana duban Nur shima ya kwaso rantsuwa yana fadin shi wlh da gaske yake...itama kuma taga alama da gasken yake dan haka ta dubi Bobby tace"yi hakuri kuje kaji?..ai nasan ba dadewa zakuyi ba ko Nuru?.."da sauri yace"eh wlh mummy nan da few minutes zamu dawo"...tace"to kaji bazaku jima ba ka daure kuje kaji?.."fuskan nan ba sarari ya mike zuwa Flat dinshi...shidai ko Allah yasan baiyi niyyam fita yau ba wlh amma shi Nur idan yaso abu kaman d’a yaso fitowa daga cikin mahaifiyarshi...kayan jikinshi yayi changing zuwa tracksuit blue ya debi wayoyinshi snn ya fita bayan ya sake feshe jikinshi da perfumes...Nur na ganin ya fito shima ya mike yayi sallama da su Mummy snn yabi bayanshi dan already har ya kusa kaiwa kofa...suna fita compound ya juya yana kallonshi fuska a cunkushe yace"sai kaje dauko motanka muje dan ni yau na sallami driver na"...Nur na sakin smile yace"dama da shiri na nazo ai..motan yana waje"...harara Bobby ya watsa mai kafin ya kama hanyar wajen...Nur yabi bayanshi yana kyalkyala daria...suna fita ya bude motan suka shiga snn ya tayar da ita ya kama hanyan college...karfe 5 saura suka shiga college amma basu karasa cikin hostel din ba sai after five...a gate din female hostel yayi parking tunda engineern yace mishi yana nan ciki...ya bude mota ya fita shima Bobby ya fito har yanxu fuskan nan a hautsine kaman wanda akaima mutuwa...shidai Nur baice dashi komai ba ya shiga ciki...basu damu da sanar da students shigowansu ba sbd ba cikin apartments dinsu zasu shiga ba dan haka kai tsaye suka zagaya ta backyard inda new apartments din suke...tun kafin su karasa suke jiyo sautin kida na tashi daga wurin amma basu kawo komai ba suka cigaba da tafia...daidai bayan apartment C suke jere kusan su goma kowacce sanye da dogon wando da t shirt amma banda Aysha dake sanyeda wata ash color jessy na manchester da wandon jessyn daya dan haura guiwarta da kadan shima ash ne da ratsin red a gefe da gefe sai kuma number 6 dake can kasan wandon...kanta ba dankwali dogon gashinta gaba daya ya sauka zuwa gadon bayanta ta maida hankalinta sosai kan rawar da take koya musu tana miming...wani kullutun abu Bobby yaji yazo ya tokareshi ya hanashi ko hadiyar yawu...duk yawan nan nasu idonshi bai sauka akan kowa ba sai a kanta nan take kuma yaji wani mashahurin kunchi yana mamayeshi...ya lumshe ido ya bude yana son yasan dalilin da yasa idonshi idon yarinyar nan sai ranshi ya 6aci...baisan meyasa kusan komai nata yake kular dashi ba...yanxu dubi yanda ta dage tana koya musu rawa kaman abunda aka turota yi makarantan knn...and the most annoying this is yanda kowa na sanyeda kayan kirki banda ita...kan kowa da akwai hula amma banda nata...gashin kowa a rufe amma banda nata snn wandon kowa har qasa ita nata sbd tsabar tsageranchi a guiwarta ya tsaya...ba kuma wanda ke sanye da kayan yan ball sai ita...shi tunda yake bai ta6ajin ya tsani kayan yan ball ba sai a kanta...sam ya rasa dalilinda yasa ya tsani ya ganta cikinsu...ji yake da yanada hali har supporting man u dinma sai ya hanata wlh sbd ba dabi’a ne mai kyau ba...Nur da tun dazu yake mishi mgn amma yaga hankalinshi bai jikinshi sai ya rungume hannunshi a chest yana kallon inda yake kalla sai yaga Lamido...murmushi ya saki yana sake kallon Bobby still yaga idanunshi kanta ko blinking bayayi kawai sai ya wuce abunshi yana daria...shidai yasan da matsala domin tun ranan da ya kwace zobuna a hannunta jikinshi ke bashi akwai gagarumar matsala amma bai nuna ba...Bobby kuwa a halin yanxu gani yake ko wanda ke prison bai kaishi baqin ciki ba...baisan meyasa ba amma tabbas yasan yana jin wani irin kunchi da 6acin ran da bai ta6a samun kanshi a ciki ba...su kuwa gaba daya ba wanda ya ganshi da haka suketa dirkan rawarsu cikin nishadi sunayi sunabin waqan...baice komai ba ya juya zuwa gidajen matrons yaci karo da wata student din yace taje ta kira mishi one of metrorin dake hostel din babu wasting of time kuwa suka dawo tareda ita...fuskanshi a gimtse muryanshi na nuna tsananin 6acin ran da yake ciki ya nuna mata su Aysha da har yanxun basu bar rawa ba yace"what’s this?..a building dina kuka barsu suke wnn lalatan babu mai tsawatar musu?.."jikin matar har ya dauki rawa tace"yalla6ai ayi hakuri za’ayi musu mgn InshaAllahu..kayi hakuri"...baice mata komai ba ya rungume hannu yana mata nuni da taje ta kirasu aikuwa ta wuce da hanzari zuwa inda suke...tana isa kai tsaye mp da suka kunna kidan dashi ta dauki tayi disconnecting nashi nan take gaba daya suka juya suna kallonta...kafin wani cikinsu yayi mgn ta nuna inda Bobby ke tsaye murya a dan kasa tace"yace a kiraku"...gaba dayansu ba wadda bata tsorata ba ganinshi a tsaye yana binsu da matsiyacin kallo especially Aysha da takejin kaman ta saki fitsari a wando don tsoro...tana daga idanunta suka hada ido dashi aiko ba shiri tayi kasa da nata tana fadin"la’ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minzzalimeen"...cikinta har wani sauti qululu ya bada sbd tsabar figici...batayi aune ba taga gaba dayansu sun nufi inda yake tsaye hankalinta ya sake tashi idonta har kawo kwalla tace"to ko hijab bazamu dauko ba?.."matron tace"wane hijabi kuma bayan ya riga ya gama ganinku a haka"...a haka suka karasa wurinshi saidai ko kallonsu baiyi ba ya juya ga matron yace mata"ki tabbata ko mutum daya bata gudu ba a cikinsu...suzo su sameni ranan monday a office dina by 4"...yana gama fadan haka ya kama hanya sabon apartment din su kuma kowacce ta bishi da kallo baki bude...masu sallallami nayi masu zaginshi ma duk sunayi haka suka mike kowa ta dauki hanyar hostel dinsu...Aysha dai ko kusa bata cikin hayyacinta dan tana ga duk cikinsu ba wadda tasan muguntarshi kaman ita shiyasa tafi kowa tsurewa a cikinsu...yanxu idan yace ya basu suspension me zata cewa Ammi da Daddy ita Aisha?...bama haka ba yanxu idan yace zai basu punishment kaman yanda ya wahalar da ita a Freedom fa?.."yanxu menene abun yi?.."ta tambayi kanta kamar tana jiran wani ya bata amsa...karashen ranar nan dai gaba daya bataji dadinshi ba dan ko baccin kirki batayi ba...Billy tun tana bata baki har ta hakura ta kyaleta.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 3208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
20
Ranan monday kiri kiri tayi kwanciyarta a hostel taki shirin shiga school din wai ita batada lafia bazata je ba...ba yanda Billy batayi da ita kan ta shirya su fita ba amma sam tace ita bata zuwa sbd tasan idonta idon proprietor ci mata mutunchi zaiyi...haka Billy ta hakura ta rabu da ita sauran da ya kamasu suna rawa tare ranan suka tambayi Billy why bata shigo school ba Billy ta amsa da batada lafia...sam basuyi tunanin da gayya tayi hakan ba so ba wanda ya sake daga maganan saidai kaf cikinsu ba wadda ba a tsorace take da kiransu da proprietor keyi musu ba..duk tsoronshi sukeji sbd bai daya daga cikin masu sakin ma yara fuska balle har suga damanshi...gashi kuma yanada wani irin kwarjini da kowane yake iya resisting idan yana tare dashi ba..yanada wani irin huge spirit dake sanya ma mutane shiga taitayinsu idan suna tare dashi...sai kuma uwa uba eyes dinshi da kowa ke fadarsu wajen nutsar da fitinanne.
Karfe biyar da wani abu ya shigo college din dan saida ya gama da Hospital snn ya taho...don ma zuwan ya kamashi dole ne amma da baiga dalilinda zaisa yashigo college monday ba tunda ba ranan shigowanshi bane...kawai ji yake idan baiga yarinyar nan yaci mata mutunchi ba bazai samu nutsuwa ba..sam bazai samu ya huce takaicin data kunsa mashi na ganinta da yayi tana rawa ba...ba ita kadai ya gani tana rawan ba amma ba na wanda ya tsaya mishi a rai kaman ita baisan meyasa hakan ba...ko don sbd tafi kowa zakewa ne oho...har yanxun ya kasa mance scene din...ya tuna ranan dinner wan Rayhan ma itace sahun gaba a masu rawa and yanada yaqinin suma itace ta koya musu...mamaki yake why yarinya kamarta take da shegen rashin ji haka..tanada fitina that yake ganin sam yafi karfin shekarunta...dukda ba sani age dinta yayi ba yasan tayi wuta takai 20 maybe ma bazata fi irin 19 ba haka...shidai da shine yake da ‘ya kamarta ko zata mutu bazai kaita karatu wani garin ba wlh sbd fitinanta yayi yawa...she is so stubborn that yake ganin aurar da irinsu kawai ya kamata ayi a huta...kai tsaye office din Nur ya nufa ya samu zai fita daga office din sbd meeting da yake dashi da entire college staff din yanxu...da mamaki sosai yake duban Bobby dan zai iya tanstewa bai ta6a ganinshi cikin college a irin wnn time din ba kuma ranar monday...komawa ciki yayi yana sake kallonshi yace"mazaa hope everything is fine?..meya kawoka college at this time?.."ta6e baki Bobby yayi yace"yaran nan na hostels zakasa a kiramin"...wara idanu Nur yayi cikeda another mamaki yace"ban gane yaran hostel ba?..wane yaran?.."tsaki Bobby ya saki cikin fara gajiya da questions dinshi yace"wadanda suka maidamin building club mana?..or are u tryinyto tell me baka gansu suna rawa ranan da muka shiga hostel din ba?.."shiru kawai Nur yayi yana kallonshi yasan definitely da akwai abu a qasa...idan ba haka ba why zaice a kirasu kawai sbd yaga suna rawa a hostel...ya bude baki zaiyi mgn Bobby ya katseshi da fadin"hold that to ur self plss...kawai kasa a kirasu kaima ka wuce meeting dinka...u are wasting our time"...wrist watch dake hannunshi ya duba yaga fa time na tafia and yanaso suyi meeting din nan dan haka ya fita daga office din yasa a kira mishi su kaman yanda yace snn shima ya shiga meeting dinshi bayan ya kudurce a ranshi sai yaji dalilin wnn abubuwan da yake.
Yana zaune office din after like 10 mins suka shigo gaba dayansu...idonshi na kansu har karaso ciki duk suka durkusa nan gabanshi yace su mike tsaye...bayan sun mike ya sake baza idanu yana son ya hangota amma sam bai ganta ba..yasan kuma zaiyi wahala idan ba da gangan tayi haka ba...bai tambayesu itaba ya shiga yi musu nasiha a nuste...gaba dayansu mamaki sukayi da sukaji ba masifa zaiyi musu kaman yanda sukayi tunani ba...nasiha ce yake musu mai ratsa jiki wanda da yawa daga cikinsu basu san there is this side of him ba sai yanxu...gaba daya kallon wanda bai san komai ba sai masifa suke mishi amma yayi proving dinsu wrong at this very moment...ya nuna musu illan da jin kida da rawa ke iya haifarwa especially gasu da suke mata snn yayi musu na killace jikinsu koda a cikin hostel ne domin kuwa ko babu maza hostel din bazaa rasa aljanu ba and gaba dayansu sun san aljanu da son mata mussaman masu kyau kyau dan haka suka dauki nasihan nashi da muhimmanchi...godia suka hau mishi bayan ya gama tareda alqawarin zasu kiyaye gaba inshaAllah...dadi sosai yaji wanda har hakan ya nuna a face dinshi ta hanyar dan murmushi daya saki and da yawa daga cikinsu was like"wow!..ashe haka smile ke mishi kyau shiyasa yakeda tsada a wurinshi?.."shidai bai sake ce musu komai ba har suka juya zasu fita...kasa hakura yayi ya dan dakatar dasu da fadin"are u sure gaba dayanku ne nan?.."wata daga cikinsu that is already crushing him tace"no sir akwai guda daya batazo ba..tana hostel batada lafia"..kanshi kawai ya iya gyada musu nan suka juya suka fita...mikewa shima yayi ya fita a office din cikin ranshi yana ayyana yanda zaiyi da yarinyar nan duk ya hadu da ita...baisan meyasa duk ta tsaya mishi a rai ba...sam ya kasa mancewa da ita duk kuma kokarin da yakeyi na ganin yayi hakan...deep down yasan ko rantsuwa yayi tana sane taki zuwa baizaiyi kaffara ba cox he is 100%sure kin fitowa tayi sbd gudun haduwa dashi...shi kanshi kuma baisan why yakeson punishing nata kan laifin da bashi ta aikawa ba...ba kuma shi zai samu matsala ba idan ma aljanu sun shafeta as result of abun da tayi...sam ya kasa gane kanshi these days...abubuwanda he don’t use to care about sun fara damunshi yanxu...sam da ba haka yake ba...yana ganin ko a titi zai ganta tana rawa bai zama lallai ya dameshi ba amma yanxu a cikin hostel dinsu ne and abun ya dameshi fiyeda tunanin mai karatu...yana karasowa ya bude mota ya shiga driver yaja ta suka fita a harabar makarantan.
Wahegari saida yayi da gaske snn ya iya hana kanshi zuwa college din don ji yake kawai idan bai ganya yaci mutuncinta ba bazai samu nutsuwa ba...amma haka ya hakura sbd gudun tarin tambayoyin da zaisha wajen Nur wanda for sure yasan bayada amsarsu...tun daga wnn ranan bai sake shigowa college ba sai ranan Thursday that is normal days daya saba shiga dama...around seven something motanshi ya shigo premises din and yana shigowa yayi nasarar ganinta zaune kan wasu chairs itada qawarta da wani da yake tunanin kilan saurayinta ne shima tunda yaga ba wai kamun kai gareta ba...daga ganin yanda suke mgn suna daria zakasan hira ba karamin dadi yayi musu b...sai Allah Allah yake suyi parking sbd ya tura a kirata yanda bata isa tayi escaping ba amma kamar ance ta juya idonta ya sauka kan motanda a kallon farko ta gane nashi ne...bata tabbatar da cewa nashin bane saida ya wuce ta gabansu taga plate number din Dr.Bobby 5 ai batasan time data mike daga wurin ta nufi classes dinsu da wani mahaukacin sauri ba kaman zata tashi sama...ta jikin mirror yake kallonta yaga yanda take ta faman sauri har tana hadawa da gudu kawai sai ya girgiza kai yana kallonta...kafin su karasa parking ya bude mota ya fito har ta shige ciki dan haka direct kawai ya wuce office dinshi...11 da wani abu ya samu call daga hospital that ana buqatarshi da gaggawa haka ya fita ba don yanaso ba driver ya daukeshi zuwa hospital din...emergency theater suka shiga and basu suka fito ba sai around 1...sallah kawai ya tsaya yayi masjid dake nan asibitin snn ya shiga mota driver yaja suka dauki hanyan college.
Daya da mintina bakwai Motan daddy ya shigo cikin haraban makarantan...wani taro ne ya kawoshi kano shine yaga before ya wuce Gombe ya kamata yazo ya ganta dan ya kwana biyu bai zo ba..ko sanar da ita zuwanshi baiyi ba sbd yanaso yaga how she’s doing a school din...dama duk zai zo bai ta6a sanar mata ba saidai kawai ta ganshi kwatsam yazo...dagashi sai driver dinshi da security guda daya...bayan sunyi parking yace da security yaje bakin gate ya tambayi masu gadi ko zasu santa dan yanata kiran wayanta bai shiga gashi kuma baiga student ko daya a premises din ba ba mamaki suna clesses dinsu...da hanzari security ya tafi bakin gate kamar yanda aka umarce shi ya tambaya ko sunsan Aysha nan sukace mai basu santa ba and abun bai sani ba shine idan zai shekara yana tambayan Aysha zasuce mishi basu santa ba because ba wanda ya santa da Aysha a cikinsu...ko yan class dinsu mantawa suke sunanta Aysha sbd yanda sunan ya 6ace 6att kowa yake kiranta da Lamido...komawa yayi ya sanar dashi sunce basu ganeta ba dan haka daddy ya bude mota ya fito yana karema premises din kallo still trying her number wai zaici saa ya sameta yanxu...daidai wnn lokacin motan Bobby ya shigo haraban school din...gefen motan daddy driver yayi parking nashi snn ya bude mishi mota ya fito...tun daga cikin mota yake kallon wnn mutumi that kana ganinshi zaka gane babban mutum ne kuma mai dattako yana tunanin me yazoyi college dinshi kuma?...har zai wuce office dinshi yaga kaman bai dace ba..bisa ga dukkan alamu mutumin wani yake nema duba da yanda yaga yanata kokarin kiran waya kuma bata shiga...juyawa yayi zuwa inda suke yana tafiya a nutse kaman yanda ya saba har ya karasa inda suke...fuska dauke da murmushi dan haka nan yaji mutumin ya mishi wani irin kwarjini yace"sorry to interrupt sir..are u looking for someone?.."murmushi daddy ya saki tareda mika mashi hannu alaman suyi musabiha yace"yarinyata nazo gani wlh kuma inata kiran wayanta baya shiga"...Bobby da yaji nauyin ya bashi hannu su gaisa yace"if babu damuwa mu karasa office dina sai insa a nemo maka ita"..daddy ya fadada smile dinshi lokaci daya yaji yaron ya kwanta mishi a rai yace"ba damuwa muje"...Bobby ya wuce gaba shi kuma yabishi baya..security dinshi zai biyosu yayi mishi alaman he should stay...suna zuwa office din ya bude suka shiga still yana murmushi ya nuna mishi sofa yace"Bismillah sir"..ba musu daddy ya zauna yana sakejin yaron na burgeshi sosai...shi kallon sani ma yake mishi sai yaga kaman ya ta6a ganinshi a wani waje...Bobby ya bude fridge ya dauko ruwa da lemo ya ajiye mishi kan table snn ya zagaya seat dinshi ya zauna ya dauki landline dinshi yace"ya sunan yarinyar da za’a kira sir?.."daddy bai maji me yace ba as hankalinshi gaba daya yana ga katon picture din Bobby dake manne a wall din office din...fuskanshi dauke da suprise look ya juya yana kallonshi yace"u mean kai son din Col Attahir ne?.."Bobby yayi shiru yana kallonshi da mamaki shima...daddy ya sake juyawa ya kalli pic din snn ya kuma juyowa gareshi har yanxun cikeda mamaki yace"ina nufin Col Attahir Waziri na Gombe..are u his son?.."a hankali Bobby ya gyada mishi kai alaman yes...wani irin bright smile ya gani shimfide kan fuskan daddy wanda ke nuni tsantsan farin cikin haduwa dashi...juyawa ya sakeyi ya kalli hoton then back to Bobby kafin yace"ikon Allah...kasan mahaifinka shine sanadiyyar matakin da nake kai a yanxu?..he was a very good and generous man..my mentor...har yanxun banida wani abun kwaikwayo kamanshi...he was a very kind hearted person..a very responsible person.."ya karasa mgnr da wnn bright smile kan face dinshi sai kuma eyes dinshi dake nuni da tsananin kewarshi da yaji sakamakon tunawa da mutuwarshi da yayi...Bobby dai mutuwan zaune yayi sai kallonshi kawai yakeyi kaman statue...wani irin qima yaji
mutumin ya sakeyi a idanunshi...kawai yaji yana sonshi sbd wnn maganganu da yayi kan dad dinshi...a rayuwa yanason ya hadu da mutumin da yasan babanshi ba don komai ba sai don kawai yayita bashi labarinshi yanajin dadi amma banda familyn dad din nashi...su wadan nan ko zasuyi me bazai iya yadda wani alaqa ya sake shiga tsakaninshi dasu ba...bayan few minutes of silence daddy yacigaba da cewa"no wonder tun a kallon farko da nayi maka naga kaman na sanka...its because kana kama da dad dinka sosai and ba iya kamanninshi kawai ka dauko ba harda halayenshi...kawai daga gani na kaji ya kamata ka taimakamin har ka kawoni office dinka without knowing who i am and wnn na daya daga cikin halayen mahaifinka...bai ta6a ganin wani na bukatar taimako bai taimaka mishi ba...ubangiji Allah ya jikanshi yasa yana aljannah"...Bobby ya lumshe ido sbd dadin addu’ar da yaji a hankali yace"Ameenn"...daddy ya zuba ruwa a cup yasha snn yace"kasan sa akwai alaqa ta sarauta tsakanin shi mahaifinmu Lamido da kakanka Waziri..wnn dalilin ne yasa dana fara aikin Custom aka hadani da mahaifin naka"...kallonshi kawai Bobby keyi yanajin dadin labarin...shi daddy yacigaba da fadin"kacigaba da irin wnn habit din yanada kyau kaji?..Allah ya maka albarka”...yana murmushi ya amsa da"Ameen..nagode sir"..daddy yace"no thanks a tsakaninmu...u are like a son to me"...sake murmusawa Bobby yayi yana shafa kanshi...tunda yake bai ta6a cin karo da mutumin da ya kwanta mishi a rai ba kaman wnn mutumin ba..da ganinshi mutumin kirki ne and he ha so much respect for him..baisan ko sbd yasan dad dinshi bane oho amma yaji yana ganin girmanshi sosai...saida ya sake daukan landline snn yace"Sir baka fadi sunan yarinyar ba"...murmushi daddy ya kuma saki yace"kaga har na manta da ita sbd tunowa da Mentor na da nayi...May his gentle soul continue resting in peace"..sake lumshe ido Bobby yayi tareda cewa"Ameen Ameen"..daddy yace"sunan yarinyar Lamido...Aysha Ahmad Lamido"...idanu a waje sosai Bobby ya dago yana kallonshi jin sunan daya ambata...he can’t believe wnn responsible mutumin shine zai haifi wnn fitinanniyar yarinyar...ganin irin kallon da yake mishi daddy yace"do u know her in any way?.."da sauri ya shiga girgiza kai yace"ah no sir..bari insa a nemota"...daga haka ya kira secretary dinshi using the landline...tana dauka yace tazo yana son ganinta...bayan ta shigo yace mata"did u know a girl called Lamido?.."secretary ta danyi shiru for the mean time kafin tace"yea na santa sir..mai kukan allura kou?.."banza yayi kaman baiji me tace ba yace"kije midwifery section ki nemota..tell her that her father is here waiting for her"..secretary ta amsa da"ohk sir"..snn ta juya ta fita daga office din...daddy ya bita da kallon jin tace mai kukan allura...knn hakan na nufin Aysha har a nan dinma kukan alluran take?..kawar da tought din yayi ya juya ga Bobby yace"kanada sister sumayya koh?.."gyada kai Bobby yayi yace"yes my elder sis"...murmushi daddy ya kuma saki yace"a lokacin bazan manta ba inajin sunanta a bakinshi...yanaji da kids dinshi sosai dan koda yaushe cikin mgnrku yake...and kanada brother mai sunan Waziri kou?.."nan ma kai ya sake dagawa yace"Sabeer"...daddy na cigaba da murmushi as old memories rush back yace"ina tunawa da sunanku ai..he was man of the people shiyasa duk na kasa dashi suke sonshi sosai"...gyada kai kawai Bobby yake yana murmushi...he doesn’t want the conversation to end.
Secretary na fita kai tsaye midwifery section ta nufa kaman yanda yace mata...duk wanda ta tambaya Lamido zaice baisan inda ta tafi ba...har class dinsu taje bata nan and gaba daya yan class din suna ciki suna lectures ita kuma ba wanda yasan inda take...gajiya tayi da neman nata ta sauka kasa ta sake dubawa nan inda classes din Nurses yake amma ba Aysha ba alamarta...tana fita daga wurin ta hangota can bakin gate ta shigo makarantan hannunta niki niki da ledoji kaman wadda taje kasuwa...da sauri ta karasa inda take tace"kece Lamido koh?.."kai tsaye ta gyada mata kai alaman eh...secretary tace"kizo office Dr.Bobby na nemanki"...Aysha ta wara idanu kaman taga abun tsoro tace"what!..ce mishi kikayi kin ganni?.."secretary bata sake cewa komai ba ta juya tace"nidai na fada miki..idan kuma inje ince mishi baki zuwa ne toh"...da sauri tabi bayanta tana turo baki tace"muje..ai dai duk abunshi bazai gutsuri naman jikina yayi pepper soup dinshi yaci ba..iyaka ya balbaleni da masifa wnn kuma shi ya sani"...secretary dai tafiyarta tayi bata ma jin abunda take fada sbd ciki ciki tayi mgnr...saida ta fara ajiye kayan dake hannunta nan kofar office din nashi snn ta tura kofar a nutse ta shiga bayan ta gama hade rai wai sbd kar ma yaga fuskanta a sake yace zai rana mata hankali...bayan ta shiga ciki ta juya tareda closing kofar tayi taking one step forward kafin idonta ya hango mata wanda ke zaune cikin office din...zare idanu sosai tayi looking at him kaman taga dodo dan har ga Allah ta dauka gizo yake mata...hannu takai ta murza idanunta sosai tana tunanin kodai sbd batasa glasses dinta bane ta fara gane gane kuma...bata tabbatar da gaske shine nan zaune ba saida taji voice dinshi na fadin"ni ne nan zaune ba daydreaming kike ba"...lokaci daya gabanta yayi wani irin faduwa irin wanda bai ta6a yin irinshi ba...juyawa tayi ta kalli Bobby taga shima idonshi a kanta snn ta sake juyowa ga daddy still shima kallonta yake fuska daure...nan take wani irin zufa ya fara keto mata...taya akai daddy yazo office din mutumin nan?..bata samu amsan tambayan ta ba ta sakejin daddy yace"ni kike jira in taso in gaisheki knn kou?.."da sauri ta karasa inda yake ta zube kan guiwoyinta murya a matukar nutse tace"daddy..barka da z..."bai bari ta karasa ba ya katseta da fadin"daga ina kike?.."wani yawu ta hadiye da kyar zufa na kara keto mata tayi qundunbala tace"da..daga class nake"kallonta yakeyi rungume da hands dinshi yace"really?..wato daga class kike?.."kai ta sake dagawa tareda cewa"eh.."sai kuma tayi saurin girgiza kan ganin irin kallon da yake mata tace"aah.."fuskanshi ba alamun wasa yace"kince eh kince aah..wanne zan dauka knn?.."hawaye na cikowa idonta tace"daddy wlh abinci naje na siyo"..yace"abinchi?..bakuda cafeteria ne cikin makarantan?.."tana girgiza kai tace"da akwai"...yace"then menen dalilinda zaisaki fita waje siyo abinci lokacinda students yan uwanki suke class..wato har yanxu baki dena irin wnn halayen ba koh Aysha?..kina ganin kaman tunda kina nesa damu you are free to do duk abunda kikaga dama kou?.."da sauri ta shiga girgiza kai tana hawaye sosai tace"daddy wlh ba haka bane...dan Allah kayi hakuri wlh Billy ce batada lafia tace in siyo mata shine na fita amma ba haka nakeyi ba wlh"...kallonta kawai daddy keyi baice komai ba...Bobby kam kusan suman zaune yayi sbd mamaki...bai ta6a tunanin haka takejin tsoron mahaifinta ba dan hasali ma shi kallon sangartatta yake mata ashe abun ba haka bane..ya tabbata da sangarta ta ake babu yanda zaayi ta shiga tashin hankali haka sbd ganin babanta...wnn kadai ya isa ya nuna cewar sam ba sangartata akeyi a gida ba kilan dai kawai halinta ne haka...amma kam albasa batai halin ruwa ba...jin kukanta ya fara cika office din daddy yace"ke denamin kuka a nana..ai bakisan da kukan ba kike aikata abunda kikaga dama sbd kinga bama ganinki kou?.."girgiza kai kawai takeyi tana kokari tsayar da kukan nata ko uffan ta kasa cewa...a dan fusace yace"bazakiyi shirun ba knn"...tun kafin ya rufe baki tayi diff kaman anyi ruwan sama an dauke...still fuskanshi a daure yace"ina Bilkisun take?.."da sauri tace"tana hostel.."yace"kun kaita asibiti ne?.."ta gyada kai tace"da safe muka kawota..an bata drugs da injections yace inshaAllah zuwa gobe zataji sauki"...gyada kanshi yayi alaman ya gamsu kafin ya sake dan hade ranshi yace"idan kin koma ki hadani da ita awaya and wlh wlh Aysha idan kika sake na gani ko naji labarin kin aikata abunda bashi kenan ba a cikin makarantan nan ko a waje Allah sai kinyi mamakin matakin da zan dauka a kanki tunda na fuskanci har yanxu akwai sauran rashin ji a tare dake..just dare me kiga abunda zai biyo baya"..kai a kasa taba matsar kwalla tace"inshaAllah zan kiyaye daddy..kayi hakuri"..baice mata komai ba ya juya yana kallon Bobby da yayi relaxing kan seat dinshi yana kallon su kaman movie..kawai mamakin yanda such a responsible and reasonable person kamanshi zai haifi tantiriyar yarinya kamar Lamido...ga dukkan alamu kuma yana iya bakin kokari kan tarbiyyarta kunnen qashi ne kawai Allah ya hore mata...muryan daddy ya dawo dashi daga duniar daya tafi da yace"son alfarma nake nema a wajenka"...wnn karon Aysha ce mai mamakin sbd sunan da taji daddy ya kirashi dashi"son dai?.."ta fada cikin ranta...murmushi Bobby ya saki cikeda girmamawa yace"ai babu alfarma tsakanimu sir..kawai ka fadi buqatarka"...shima daddy ya saki smile din jin dadi snn ya nuna Aysha da har yanxu ke zaune kan guiwoyinta yace"so nake kasamin ido a kanta plss..tanada fitina sosai..she is so stubborn that saida mahaifi na yasa baki before in amince ta taho karatu wani garin..batajin mgn sam kuma tun tana karamarta haka take...na yadda da tarbiyyarka shiyasa zan dora wnn responsibility din a kanka and inada tabbacin u can do it...i want u to put eyes on her idan kaga zata aikata abunda ba daidai ba kayi stopping dinta snn duk lokacinda kace tayi wani abu batayi ba just give me a call zakaga hukuncin da zanyi mata..i hope u can do that for me"...gyda kai Bobby yayi yace"inshaAllah sir"...murmushi daddy ya kara saki tareda mikewa ya isa gaban table dinshi ya mika mishi hannunshi yana cewa"thank u so much son..ubangiji Allah jikan mahaifinka"...Bobby da kunya ya hanashi mika nashi hannun yace"Ameen sir"...kamo hannun nashi dady yayi tareda shaking da nashi still smiling yace"we’ve already became family so meye na makale hannun?.."murmushin dai ya kara saki kanshi kasa ya kasa hada ido dashi...hakan da yayi ya sake burge daddy sosai ya kuma tabbatar da cewa ya damka amanar Aysha a hannun daya dace domin yasan har abada jinin Attahir bazai ta6a kasancewa bata gari ba..ya aminta da tarbiyyar yaron dari bisa dari...bayan ya saki hannun nashi ya zari card dinshi daga aljihu ya ajiey kan table dinshi tareda fadin"here is my card ka kirani da wuri sbd inyi saving numberka"..Bobby ya dauki card din yana fadin"InshaAllah sir..thank u so much"..daddy yace"always welcome son..will like to meet u again"...yace"inshaAllah Sir..Allah ya tsare"..daddy ya amsa da"Ameen"..kafin ya fita daga office din...hajia Aisha kuwa suma ne kawai batayi ba tsabar mamaki...har yanxu ta kasa fahimtan ta inda wnn sabon alaqa ya 6ullo tsakanin daddy da inyamurin mutumin nan..sam hakan bai gamsheta bane..dr Bobbyn da ba kaunarta yake ba shine yanxu zaa ba amanarta aikam tasan ta gama yawo..takura dai iri iri zata sha a wurinshi kuma batada bakin complain tunda umarnin mahaifinta ne...ficewa tayi itama yabi bayan daddy...yana dab da shiga mota ta cimmasa dan haka ya dakata tareda juyawa gareta ya zaro kudi masu yawa daga aljihun babban riganshi yayi dividing kudin into two tareda mika mata daya yace"ga naki"...ta amsa tana godia snn ya sake bata dayan yace"wnn kuma na Bilkisu..saura kuma ki bari inji labarin ya saki ko ya hanaki wani abun kinki yi zakiga yanda zanyi dake"...kasa cewa komai tayi kanta kasa...security dinshi dake tsaye ya nunama ya dauko mashi wani abu a mota nan da nan ya bude motan ya dauko wani bag mai kyau ya mika mashi...daddy ya amsa tareda mikawa Aysha dake tsaye kai a kasa yana cewa"take.."da sauri tasa hannu biyu ta karba tareda dan risinawa tace"Allah ya saka da alkhairi "..a hankali yace"Ameen"..snn ya shiga cikin mota...ta matsa jikin window tana dubanshi tace"daddy Allah ya kiyaye hanya..ina gaida su Ammi"..yace"zasuji inshaAllah..ki koma ciki"...a hankali tace"toh.."tareda barin wurin...tana kallo motan nashi har ya fita daga makarantan ta sauki ajiyar zuciya tareda dafe kirjinta da har yanxu bai dena bugawa ba...taso komawa ta dauko kayan data bari a kofar office dinshi amma bazata je ba haka kawai yayi ram da ita a wajen...yanda yake neman tan nan tasan ai idan suka hadu rashin mutunchi ne zata sashi musamman yanxu da daddy yace wai yasa mata ido...wucewa tayi class dinsu cikin ranta tana ayyana wai ita daddy zaice a sa mata ido sai kace wadda take aikata wani aikin ashsha.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
21
Tun daga wnn ranan bata sake yadda ta hadu dashi ba har tsahon sati guda shima kuma bai nemeta ba...gashi duk sukayi waya da daddy sai jaddada mata tayi mishi biyayya and ta ringa zuwa tana gaisheshi time to time ta amsa mishi ai already tana zuwa...gaba daya haushi takeji that daddy zai dinga hadata da wnn mutumin...ko a inama ya sanshi har ya yadda dashi haka oho?.
Yau Thursday suna zaune class dinsu tana koya ma wasu assignment kiran daddy ya shigo wayanta...excusing kanta tayi tareda daukan wayan tana gaisheshi..bayan ya amsa yace mata"where are u now?.."tace"ina class daddy"..yace"kinje kin gaida Attahir?.."shiru tayi tanaso ta gane waye Attahir yace"ur proprietor"...da sauri tace"eh..aah banje ba..amma zanje sai mun tashi daga class"..yace"to idan kinje ki hadani dashi a waya"..bai jira cewarta ba taji ya kashe wayan...tabi wayan nata da kallo tana mamakin abunda yace..tadai san bai yiwuwa ace har yanxu Bobby bai kirashi don akan idonta ranar yace yanaso ya kirashi a wuri so dole yanada number dinshi amma why zaice ta hadasu a waya?.."so yake ya tabbatar da kina zuwa gaidashi ko bakiyi"..cewar wani 6angare na zuciyarta..ta kuwa yi na’am da haka don dai tasan zaiyi wahala ace kiran wayanshi yayi bai shiga ba...komawa tayi suka karasa assignment din kafin lecturer dinsu ya shigo ta nufi office dinshi don tasan idan bata hadasu kamar yanda daddyn yace ba then zasu samu matsala gagaruma...tana isa bakin office dinshi kafin ta shiga secretary dinshi ta bita da wani irin kallo tace"wai ke me kike zuwa yi office din nan ne?.."wani kallo Aysha tabita dashi irin na rainin hankali kafin taja tsaki ta wuce...da sauri ta mike daga inda take tana fadin"ki bari a fada sanar dashi zuwanki kafin ki shiga"...ai ko tsayawa sauraronta batayi ba ta banka cikin office din itama tabita da sauri...tana shigowa secretary din itama ta shigo da surinta...Bobby dake zaune seat dinshi ya daga idanu yana kallonsu..ganin yanda kowacce ke huci yace"bakuda hankali ne?..why zaku shigomin office kai tsaye haka without my permission?.."da sauri secretary dinshi tace"Sir cewa nayi ta jira in fada maka idan kace ta shiga sai ta shigo shine taki tsayawa ta shigo ciki"..juyawa yayi yana kallon Aysha data wani hade rai yace"kan wane dalili zaki shigomin office kai tsaye?..are u mad?.."sake daure fuska tayi tana turo baki tace"raina min hankali zatayi shine kawai na shigo"...tsaki ya saki tareda juyawa ga secretary dinshi yace mata"u can leave"...ba musu ta juya ta fita daga office din...shi kuma ya maida dubanshi gareta fuskanshi cunkus yace"wato ke bazakiyi hankali ba kou?..duk wani abu da bai kamata ba bazaki dena yi ba kou?.."turo baki ta sakeyi tace"Sir ni me nayi?.."kallonta kawai yake yace"oh tambayana ma kike?..to bari na kira mahaifinki na sanar dashi shi sai kiyi masa bayani"...ai tun kafin ya karasa ta karasa kusa dashi da sauri tace"aa dan Allah kayi ban karawa"..harara ya watsa mata bai sake cewa komai ba...ita kuma taja kujera zata zauna yayi saurin katseta da fadin"who asked u to sit?.."ta wani marairaice tace"Sir dan Allah..daddy ne yace in hadaku a waya"...still bai sake cewa komai ba ita kuma ta zauna snn ta fiddo wayanta tayi dialing number daddy...yana fara ringing tasa a speaker snn ta mika mishi...ya kar6a ya wani 6alla mata harara tareda cirewa daga speaker snn yakai kunnenshi..tana ganin yanda har wani sunkuyar dakai yake yayinda suke gaisawa da daddyn...ta lura he have so much respect for him and hakan ko kadan bai burgeta ba don gani take duk ladabin kura ne...saida suka kammala wayan snn ya mika mata abarta yana hararanta yace"wato ce masa kikai kina zuwa gaisheni koh.."sake turo baki tayi tace"ai daga yanxu zan fara zuwa"...ya wani ta6e baki yace"kiyi zamanki bana bukata..now tashi ki bar min office"...mikewa tayi ta sake hade rai fa fita cikin ranta tana ayyana shegen son office inda kasan kanshi aka fara zaman office...komai sai ya wani ce office din,my office sai kace wani yace ba office dinshi bane...batafi 10 mins da fita ba Nur ya shigo office din...ya karasa ciki ya zauna yana duban abokin nashi yace"maza yane?.."Bobby yace"normal..kwana biyu..ya aikin"..yace"aiki fine yanxu ma mgnrshi ne ya kawoni"...Bobby yace"umhum inajinka"..."kan batun Festivities din nan ne"...gyara zama Bobby yayi before saying"ina sane dashi ai..next week za’a fara kou?.."Nur yace"yea and yanxun nayi receiving message daga social department that suna buqatar additional money for the preparations"...buda hannu Bobby yayi yace"then ka basu mana"...Nur yace"dama in fara mgn da kai ne..if kace a basu sai a basu"...wani kallo Bobby ya shiga binshi dashi kafin yace"seriously?..haka ka daukeni dama?..kenan har yanxun ban wuce wnn matsayin a wurinka ba?.."shafa kai Nur yayi yace"sam ba haka bane..kawai dai naga bai kamata in fara amsan kudi without permission dinka ba"..yana rufe baki Bobby yace"gaskia bakayi min adalci ba idan har yanxu baka bar irin wnn tunanin ba..now tashi ka bar min office"...dan murmushi Nur ya saki saying"abun hadda kora kuma?.."Bobby yace"yes tunda baka daukeni bakin komai ba ai banga amfanin zamanka nan ba so kindly leave"..gyara zama Nur yayi hade da fadin"to kayi hakuri ya wuce"...harara ya sake 6alla mishi shi kuma yasa daria yace"da gaske bazan karaba mana..sorry".
Ranan Friday akayi pasting result dinsu na first semester wurin ya cika fam da jama’a kowa na kokarin duba nashi wanda sukayi passing mata murna while masu resitting suna jimami...Aysha dai na kwance a hostel dan ko fitowa batayi ba sai Billy ce tayi kokarin duba musu da taimakon Sa’eed sbd turereniya akeyi sosai a wurin...bayan ta samu fitowa daga hayaniyar ta samu waje ta zauna tareda dialing number dinta...cikin muryan bacci ta daga da fadin"Hello"..Billy tace"so u are still sleeping"..tace"eh mana ban dade ma da kwanciya ba"...cikin excitement Billy tace"anyi pasting results yanxun nan and gues what?.."a hankali tace mata"what?.."da sauri Billy tace"as usual ke kikayi overall..and this time around bestynki ma yayi abun kirki"...daria ta saki dukda baccin dake idonta tace"kema dai kinsan my besty is always intelligent kece dai kawai baki ganin haka"...ta6e baki Billy tace"oho ku kuka sani..am hanging up now"..da sauri Aysha tace"wait..baki fadamin naki ba ai"...wani murmushin Billy ta saki kafin tace"congratulations to me..inada 4.55"..tun kafin ta rufe baki Aysha ta saki wani ihu tana fadin"are u serious Billy?..gaskia am very happy bari in kira besty this calls for celebration"...murmushi Billy ta kara saki tana jin yanda take farin ciki ko nata result din bataima wnn murnan ba koda yake idan da sabo ai ya kamata abun ya zaman mata jiki dan tun shigowarsu college din bata ta6a scoring below 5 points ba...kafin ma ta jira jin ta bakinta tayi hanging kiran and for sure tasan bestyn nata zata kira kamar yanda ta fada.
Bobby da bai samu shigowa college din da wuri ba sai after jumu’at prayer motanshi na shigowa ya hangi crowd din dake wajen sai ya tuna ashefa Nur ya fada mishi cewa yau zasu kafe result...daga dan gaban inda aka kafe result din ya hango katon banner da suke kafewa duk shekara na best students of the year kowa da grade dinshi da department sai kuma picture dinshi a jiki...driver bai karasa inda ya kamata yayi parking ba yace ya saukeshi nan wurin..ba musu yayi parking daga gefe kafin ma yazo bude mishi kofan ya bude ya fita...inda aka manna babban banner ya nufa...haka nan yaji yanason ganin da akwaita a jiki ko babu...aikam yana karasa yayi ido biyu da pic dinta tana sanye da uniform da glasses dinta a ido...qasan pic din nata ya kalla baisan time daya wara idanu yana sake kallon points din nata ba...gani yake kaman karya ne bazata iya scoring wnn points din on her own ba...hoton su biyu ne kadai a jikin banner daga ita sai Sa’eed da yayi overall a Nursing department...dukda baisan yaron ba amma ya jinjina mashi sosai dan points ba kadan ba shima yakeda...ita kuwa nata har yanxun bai gama yadda ita taciyoshi da kanta ba...bayan ya gama kallon ya shiga takawa a nutse zuwa office dinshi saidai kafin yakai office din kusan mutum uku sukazo suna gaisawa dashi snn suka nufi office din tare...deep down wani irin feeling yakeji...like gaba daya sai baiji dadin ganinta da yayi jikin banner ba...not because yana mata bakin ciki but because yana ganin yin hakan kaman talla ne akeyi da ‘ya’yan mutane tunda yasan yanxu duk wanda ya shigo college din sai ya gani and hakan will make her popular da bai zama lallai parent inta su so haka ba..especially ita da dama ba wani cikakken nutsuwa gareta ba...ya fuskanci kanta na rawa shiyasa ko mahaifinta baya sassauta mata...har ya isa office dinshi bai bar tunanin ba and yanaso yayi ma Nur mgnr kuma yanajin tsoro kar yazo yayi misquoting dinshi amma seriously baiji dadi ba sam...sai yakejin kaman yaje ya yageta daga wurin amma ba hali...hakura yayi da yima Nur mgnr saidai ya kudirce a rai kafin next year zai samu yayi mgn dashi kawai a hakura da banner ma gaba daya...sam baiga amfanin yin hakan ba...dukda ba yanxu aka fara ba amma wnn karon kam abun baiyi mashi dadi ba.
Shirye shirye sukeyi sosai for the upcoming Annual Festival da ake gabatarwa cikin college din every year...shiri ba daga 6angaren students ba ba kuma daga 6angaren social department ba...week guda suke cinyewa suna abu guda and wnn year din ma kaman ko wacce shekara sun gama tsara duk yanda festivities din zasu kasance...ranan farko daya kama Monday zasu gabatar da dramas da wasu daga cikin students din zasu gabatar..da akwai English drama sai Hausa drama...rana na biyu kuma zasuyi cultural activities rana na uku ne ake inviting mawaqa daban daban suzo suyi performing a wurin sai rana na hudu wich is Thursday zasuyi Public Lecture and Fun Walk ma’ana za’ayi picking one among cututtuka da suke damun mutane a wnn lokacin sai daga cikin doctors da ake inviting zuwa wurin suyi fashin baqi akan cutan bayan an gama sai su fita fun walk dasu police bands da masu dj suna tafe suna waqa da rawa zasubi ta cikin gari har zuwa state road snn su dawo college din a qafa...ranan Friday wich is the last day of the festival sukeyin sport activities such football,volley ball,table tennis,snooker,basket ball dama sauran wasanni na maza dana mata.
Ranan Monday wich is the first day if the festival wurin 10 na safe auditorium dinsu na cike da students,doctors da kuma manya manyan baqi from every angle na kano da akayi inviting dinsu...kowa yana zaune a respective wurin da aka tanadar musu...mike na hannun mc yanata welcoming baqi tareda sanarwa cewan a jira wanda zasu gabatar da drama zasu bayyana in few minutes time...daga can waje masu yin draman ne a tsatsaye suna mgn da wani daga cikin organizers na festivals din...ba anko sukayi ba amma kowa cikin yayi kyau in his own way...saida ya gama musu karin bayani kan abunda zasuyi snn yace su shiga audit din...suka jera kansu a layi snn dj yasa musu waqa suka fara shiga wurin...Aysha na tsaye a gaba tana rikeda katon sign board da aka rubuta day 1 English and Hausa Drama...suna shigowa wurin ya kaure da sowa da tafi kowa sun burgeshi...Dr.Bobby dake zaune inda aka tanada domin shi a hankali ya dago idanunshi ya kallesu...as always idanunshi ita suka fara hango mishi...tana sanye cikin riga da straight skirt na atampa red da touches din black leaves a jiki...ta daura dankwalinta irin daurin da ake cewa Zara Buhari ta fito da gashinta ta qasan daurin snn ta kalmasheshi ya tsaya a wuyanta...daga bayan skirt din nata an dan tsagashi kadan ta kasa sbd yayi mata dadin tafia...takalmin kafanta flat ne sosai black sai veil dinta da tasa a kafadanta shima black...sai wrist watch da dankunnenta suma black...batasa sarqa ba dan haka fair wuyanta yana nan sai daukan ido yake...a hankali take takawa tana rikeda sign board a hannunta sai murmushi take dimples dinta na fitowa...wani irin abu yaji ya taso tun daga kwakwalwarshi yazo ya tokare mishi maqogaro shi bai tafi ba kuma shi matsa ya bashi sararin maqogaron ba...tunda yake bai ta6a tsintar kanshi cikin 6acin rai irin wnn ba..har wani zafi yaji yana rufeshi duk kuwa da sanyin ac dake wurin...lokaci daya kanshi yayi wani mugun sarawa kaman zai tarwatse..har yanxun kuma ya kasa dauke idonshi daga gareta har suka karasa suka zauna...lumshe idanunshi yayi yana karanta innalillahi a cikin ranshi wai ko zai samu sassauci...kai tsaye kuma yace ga abunda ke damunshi bazai iya ba dan shi kanshi bazaice ga dalilin wnn sudden change din nashi ba...sam baisan yaya zai misaltashi ba...kokari yayi sosai yayi kokarin danne abunda ke taso mishi ganin har za’a fara taron...yana kallo aka fara kiran sunan wanda zasuyi draman kawai ya runtse ido yana addu’a Allah yasa babu ita a ciki saidai kamar jiran addu’an nashi akeyi yaji mc na kiran "Aisha Ahmad Lamido"...sake runste idanun yayi yanajin wnn kuncin da yaketa kokarin 6oyewa yana sake neman hanyar dazai fito amma bai bashi dama ba dan kara dakewa yayi sosai wnn karon har yana dan muzurai snn ya bude idon...baisan ko shi yake kai idanunshi gareta ko kuma idanun ne ke kai kansu gareta ba dan yanxun ma ita ya sake gani bayan ya bude idon...karasawa sukayi suka zauna inda aka tanada domin yin draman...acting zasuyi itada Sa’eed matsayin mata da miji Billy kuma kishiyarta a cikin sauran kuma akwai yara snn akwai set of another couple da dai sauransu...cikin kwarewa da nutsuwa suka fara gabatar da draman nasu na English knn...wurin sai yayi tsit banda voices dinsu ba abunda akeji...gaba daya sun saki jiki suna acting dinsu sosai dan babu wanda zai gani yayi tunanin ba gaske bane sai wanda ya sani...dama kuma sunyi rehearsal sosai shiyasa basu samu wani problem ba...Bobby kuwa tunda yake bai ta6a sanin da akwai kunchi irin wnn yakeji a yanxu ba...kallon yanda suke acting itada Sa’eed kadai yasa yaji kaman zazzabi na neman kamashi...baisan meyasa yake feeling what he’s feeling ba...baisan why zai damu da rayuwar yarinyar nan ba..."sbd amanarta da mahaifinta ya baka"..cewar wani sashe na zuciyarshi...babu wata wata kuwa yayi na’am da wnn amsa don yasan da gaske kuwa ba abunda ya hadashi da ita bayan wnn...da wnn amsa na zuciyarshi ya dan samu sauki kadan daga cikin abubuwanda ke damunshi...haka yacigaba da daurewa yana kallonsu har wani murmushin yake yakeyi sbd kar mutane su dago halin da yake ciki...draman nasu ya dauki kusan one hour kafin su gama...wanda zasu gabatar da na Hausa akace su zama ready kafin mc yacigaba da surutanshi...sauran kuwa tafi aka shigayi musu sosai dan ba wanda basu qayatar ba a wurin Bobby kam shi kadai yasan halinda yake ciki...bayan lokaci mai tsayi masu draman Hausa suka shigo and to his biggest suprise wnn karon ma da ita a ciki...lokaci guda face dinshi ya sauya yana kokarin mance jarumtar da yace zai nuna...wnn karon kuma matsayin budurwar wani ta fito hakan kuma ya 6ata masa rai fiyeda tunaninshi...haka nan ya sake daurewa ya kalla har suka gama amma fa kafin a gama ya saki tsaki yafi cikin carbi...6acin ranshi kuwa ya ninka na dazu ninki ba ninki...gaba daya yaji zaman wurin ya gallabeshi burinshi kawai a tashi ya samu yarinyar can ya zabga mata rashin mutunchi...kwata kwata baisan dalilinda yasa bayason ganinta cikin irin wadan nan abubuwan ba...bayan sun gama masu jawabi duk suka tayi sukayi kayansu...wanda zasu bada kyauta ma duk suka bayar and Lamido na daya daga cikin wanda suka samu kyautar 50k da wani attajirin mutumi ya bayar...ran Bobby idan sun kai dubu duk a 6ace suke...ji yake inama yanada hali ya kar6e kudin daga hannunta gaba daya sai yaga ta gidan uban da zatayi amfani dashi dan yaga sai wani fara’a take tana jujjuya ido ita bata yadda ba celebrity...InShot har aka tashi daga wajen Bobby baisan ina kanshi yakeba...a zafafe ya koma office dinshi ya dauki waya da niyyan kiran secretary dinshi tasa a nemo mashi ita nan take kuma wani tunani yazo masa..."to idan na kirta ince mata me?.."ya fada a fili kaman he’s talking to someone...nan take kuma ya shiga girgiza kai yana fadin"no yanxu idan na fadi wani mgn tana iya misquoting dina ma tunda ba hankali gareta ba"...ya sake fadama kanshi...can kuma yace"amma ai sbd babanta zanyi hakan kou?.."yayi shiru kaman yana sauraran amsan da zuciyarshi zai bashi kafin yace"No I won’t talk to her...wai ma ina ruwana da ita taje taita haukanta mana is not as if i care"...ya fada yana daddaure face dinshi kaman tana zaune nan kusa dashi...da wnn shawara yayi amfani don bai kiratan ba a cewarshi wai baison raini...haka yayi dakon bakin cikin daya kwasa ya kaishi gida su Mummy sukaita aikin fama.😹
The next day kasa fitama yayi da wuri sbd tunanin abunda zuwan nashi zai haifar...yadai san a yanda take da shegen rawar kai yanda tayi performing a komai na jiya yau din ma zaiyi wahala idan batayi performing ba..shi kuma baisan meyasa yakejin abunda yakeji ba and Allah ya sani bazai iya kiranta ya hanata ba sbd kar tayi tunanin wani abun daban...da yanada ikon hana kanshi jin abunda yakeji da ya aikata hakan wlh ko don ya samawa kanshi salama amma bayada damar hakan...wnn dalilin yasa bai samu fitowa ba har saida yaga Nur ya fara kiranshi a waya and yasannshi da shegen naci haka zaiyita jera mishi kira idan har ba fitan yayi ba.
Wani daki ne kusada auditorium dinsu inda daya wanda zasuyi performing suke ciki kowa yana karasa shiryawa...cultural dance suka shirya na Hausa,Fulani,igbo da kuma yoruba...and kowa daga cikinsu yana sanye cikin traditional attire na tribe da zaiyi representing...Lamido sarkin rawa zatay participating kusan gaba daya sbd ita koya musu rawar...da farko cewa tayi only Fulani da Yoruba zatayi sai hod na social department dinsu yace tayi participating gaba daya...Hausa Dance shine na farko dan haka koda mc ya kira iya wanda zasuyi hausa dance din ne suka fita daga dakin...as usual itace a gaba tana rikeda sign board kaman najiya saidai shi an rubuta day 2 cultural activities...wata kuma daga cikinsu ta rike wani da aka rubuta Hausa Dancers a jiki...waqa aka sakar musu ta hausa mai dadi yayinda suke shigowa cikin wurin...gaba dayansu suna sanye cikin normal dogon riga na atamparsu iri daya kowacce ta daura dankwalinta babu mai mayafai cikinsu...bayan sun karasa dance floor sun tsaya dj ya samo waqar hausa ta gargajiya yayi playing snn suka fara dancing...yau ma Bobby yana zaune mazauninshi na jiya and gaba daya tunda ya dora idonshi a kanta ya samu gagarumar matsala don komai nashi tsayawa yayi cak banda zafi ba abunda yakeji har cikin heart dinshi...lumshe idanunshi yayi yana salati dan abunda yake jin yaji jiya was nothing compared to what he is feeling right now...ji yake kaman yaje ya dauketa ya fita da ita daga wirin...haka nan yakejin ciwon kallon da mutanen wurin zasuyi mata tana rawa kamar batasan ciwon kanta ba.
Rano✨
Wnn littafin na kudi ne ban yadda wani ko wata ya fitarmin dashi ba...masu buqatan siya zasu tura 300 zuwa 2208991344 Aisha Ahmad Tijjani Zenith Bank...sai a tura evidence of payment via 07063800556.
22
Ranshi bai sake 6aci ba saida yaji yanda gaba daya wurin ya kaure da tafi da sowa ana hailing dinsu..nan take yaji wani abu yazo ya tokare masa wuya...abun bai tsaya haka ba har liki mutanen da akayi inviting suka fara tasowa suna musu...bayan sun gama aka kara tafa musu sosai snn suka fita mc yacigaba da zance kafin next dancers su fito...dakin da suka shirya suka koma nan kuma suka fara arranging next dancers da zasu fita wato Yoruba Dancers...Lamido ce kadai tayi changing dress dinta zuwa na yoruba snn ta shiga cikin sauran suka koma ciki...suma dai da tafi da sowa akayi welcoming dinsu...Dr.Bobby yana zaune sam baiyi mamakin ganinta ba dan yasan dama hakan zai faru saidai bai saniba ko zai iya cigaba da jure abunda yakeji har su gama...yau dai ya rantse kome zai faru sai yayi mata mgn saidai idan taga dama misquoting din nashi he no longer cares..kawai haushi yakeji that gaba daya festival din ma ya fita daga kanshi kuma ya rasa wnn masifa da akan yarinya guda daya yana neman rasa sukuni da nutsuwarshi...suna isa dance floor aka sa musu waqan yoruba suka fara dancing...tafi da sowa kam sun shashi kaman ba gobe ga kuma ruwan kudi da suka samu daga mazauna wajen...lokacin da suka fito zasuyi na igbo Bobby kasa dauke ido yayi a kanta sai yaga kaman duk kayan da ta saka ba wanda yayi mata kyau kamansu...baisan ko don shi ya kasance igbo din ba amma kayan sun amsheta kaman itama igbo din ce...sai yaga kaman idon kowa na wurin a kanta yake sbd kyawunda tayi...bata sake bashi mamaki ba saida suka fara rawar...sunyi kokari matuka kaman dama inyamuran ne su...har yanxu kuma wnn zafin da yakeji yana nan wanda shine yasa gaba daya baya enjoying zaman wurin...Fulani dance shine na karshe and lokacinda suka shigo Bobby baki da hanci ya saki yana kallonta...tunda yake bai ta6a tsaywa ya kalleta irin na yau ba...tayi mishi kyau fiyeda yanda bakinshi zai iya fada..shi baima ta6a ganin kyanta kaman na yau ba tunda ya santa...haka akasa musu waqar fulani sukayi rawa sosai yanda ya kamata...and again an watsa musu naira snn wani babban mutumi dake wurin yayi musu kyautar kudi masu yawa...wani kuma daga cikin baqin shima yace ya bawa Aysha kyautan sabuwan waya Smsung Galaxy...farin ciki sosai takeyi har hakan ya kasa 6oyuwa dan sai murmushi takeyi Bobby kuma kamar bala’i idanunshi suna kanta yana ganin yanda dimples dinta ke fitowa as a result of smile da take...kasa cigaba da zaman wurin yayi kawai ya mike kaman wanda yakeda mutanen 6oye ya fita daga hall din kusan gaba daya mutane suka bishi da kallon mamaki...Nur ne ya mike da sauri yabishi a baya yana dab da shiga office dinshi ya iskeshi yace"Bob are u alright?..lafia naga ka tashi ana taro ko wani abun ya faru ne?.."juyawa yayi a fusace yana kallon Nur din snn ya nunashi yatsa yace"Fuck you"..daga hakaya bude office dinshi ya shiga ciki tareda bugo kofar da karfi...Nur mutuwan tsaye yayi a wurin yana kallonshi da mamaki...to meya sameshi haka?..kodai wani saga ciki guests din yayi mishi abu?..duk kokarinshi na yaga yayi pointing finger kan dalilin tasowarshi daga wurin ya kasa...baiyi yunkurin binshi cikin office dinba kawai ya juya tareda komawa can wurin still yana tunanin abunda akai mishi.
Bobby na shiga office din ya zauna tareda dora kanshi kam table yana sauke numfashi da sauri kaman wanda yayi race...ko kusa baya son wnn sabon al’amari dake kokarin kunnowa cikin rayuwarshi..bayaso sam...baisan kan wane dalili zai dinga jin haka akan yarinyar da bai hada komai da itaba...shi tunda yake ma bai ta6a samun kanshi cikin yanayi irin wnn ba sai yanxu...gaba daya yarinyar nema take ta zame mishi tauraruwa mai wutsiya...ciwo yakeji sosai na raye rayen da taje tayi a bainan nasi..kuma sbd rashin sanin darajar kai ko dan mayafi bata yafa ba ballantana ayi mgnr hijab..gaba daya ya kasa gane wace irin yarinyace ita?..duk sai yaji kaman bai kyautawa babanta daya damka amanarta a hannunshi ba...kaman wanda akama allura ya mike da sauri ya fita daga office din...can inda audit din yake ya nufa yana shiga premises din wurin yaga Billy ta fito daga ciki tana waya tana ganinshi tayi saurin kashe wayan da takeyi tana kallonshi a tsorace...voice dinshi a cunkushe yace mata"where is ur friend?.."da sauri ta nuna auditorium din tana cewa"tana..ciki"..."go and call her"..ya fada hands dinshi zube cikin aljihu...ba musu Billy ta juya da sauri ta koma ciki...can tsakiyar dance floor ta hangota bayan sun gama performance dinsu aka sakar musu kida suka fara rawa gaba dayansu...haka Billy ta kutsa ta cikin mutane zuwa inda take kawai sai ji tayi ta kamo hannunta ta shiga janta...Lamido ta kwace hannunta tana turo baki tace"Billy rawa nakeyi dan Allah"...harara me kyau Billy ta watsa mata before tace"to kicigaba da rawa ai ga Proprietor can yana nemanki"..bata rufe baki ba Aysha ta zaro idanu tana fadin"dan girman Allah da gaske?.."kama hannunta Billy tayi suka fita daga wurin snn tace"Allah da gaske nake..yana can a waje fuskan nan kaman bai ta6a daria ba dan wlh har tsorata nayi dana kalleshi"...nan take hankalin Aysha ya fara tashi tace"na shiga uku meyasa yake nemana kuma?.."Billy tace"indai kinsan bakiyi laifin komai ba ki kwantar da hankalinki..kiyi addu’a kije ki sameshi in Allah ya yadda ba abunda zai miki"...girgiza kai kawai Aysha keyi tace"zo muje ki rakani dan Allah"...Billy ta kwalo idanu waje tana fadin"Ni?...rufamin asiri Lamido in mutu maza su kaini ba mata ba...haka nan inje yayita zazzaro idanun nan nashi yasani sakin fitsari a wando"...dukda tashin hankalin da take ciki saida mgnr Billy ya sata daria...sai kuma ta marairaice fuskanta tace"na shiga uku tsoron zuwa nakeyi wlh...nasan yanxu abu karami yake jira ya hadani da daddy"...Billy tace"ba fada miki inshaAllah ba komai kedai kawai kije kiji mezai fada idan ba so kike ki kara wani laifin ba"...jiki a sanyaye ta gyara mayafinta snn ta fita daga wajen...bata sameshi nan waje ba dan haka ta wuce office dinshi...tana shiga ya dago fuskanshi da yayi murtuk kaman na marasu imani kawai ya mika mata hannunshi murya a cushe yace"bani wayarki"...mika masa wayar tayi da sauri tareda sunkuyar da kanta kasa tana wasa da fingers dinta...shi kuma yana amsan wayan yasa digits dinshi snn yayi dialing...wayanshi dake ajiye kan table dinshi yayi ringing alaman kiran ya shigo snn yayi quitting call din tareda ajiye wayan a kusada nashi...Aysha dai har yanxun kanta na kasa tana kwararo mishi addu’a cikin zuciyarta...tsoronta Allah tsoronta kada ace wani laifin tayi ya kira daddy ya fada masa...shi kuwa kallonta yakeyi yanajin tamkar ya kwada mata mari don haushi..dubi dai yanda ta wani nustu a gabanshi kaman mutumiyar kirki amma dazu taje ta gama bayyanar da jikinta wa mutane suka kalla...ko rantsuwa yayi yasan da kyar babu wanda bata burgeba a cikin wadanda suke wajen...kawai ciwo yakeji that a gaban idonshi abun ya faru and he couldn’t do a thing...cikin muryan daya kusa sanyata fitsari yace"wato ke bakida hankali kou?..sbd bakisan ciwon kanki ba kikaje kina rawa gaban mutane kina musu tallan jikinki kou?.."dan dagowa tayi ta kalleshi kafin ta mayar da kan nata da sauri dan tsoro idanun ma suka bata...saida ta dan marairaice snn tace"tallan jikina kumah?.."a fusace yace"if u dare say another word a wurin saina kwada maki mari...tambayana ma kikeyi sbd bakida kunya kou?.."shiru tayi tana turo baki...yace"well let me call ur Father and tell him all you’ve been doing"..yana karasa mgnr ya dauki phone dinshi dake nan kan table ai batasan time din da ta kama hannun nashi ta rike gam ba sbd tsoro...cikeda tashin hankali tace"Sir dan Muhammadu rasulillahi kar ka kirashi..i beg of u please"..ta karasa mgnr hawaye ba zubowa kan cheeks dinta...Bobby dake kallon yanda ta rike mishi hannun yace"how dare you?.."sakin hannun nashi tayi da sauri tana cewa"am sorry...Sir dan girman Allah ka rufamin asiri karka fada wlh fada zaiyimin"...sake daukan wayan yayi yana searching contact din daddy yace"da kina tsoron fadan ai bazaki aikata abunda ba daidai ba"...wnn karon hannayenta ta hade waje daya in a pleading tone tace"Sir na rantse da Allah ban karawa kayi hakuri plss"...ajiye wayan yayi yana kallonta..dama baida intension din kira yayi haka ne kawai dan ya tsoratata tunda already yasan yanda take tsoron mahaifinta...idonshi a kanta yace"fadamin meyasa bakijin magana?.."tana cigaba da hawaye tace"am sorry"...yace"ba wnn na tambayeki ba..i said meyasa bakyajin mgn?..why kikeda fitina?.."shiru tayi tana goge hawayenta sai can kuma tace"nima ban saniba"...tsaki ya saki tareda daukan wayanta yana mika mata yace"leave my office immediately..and if u like gobema kizo kiyi abunda kikayi yau kiga idan ban sanar dashi ba"..kar6an wayan tayi tana turo baki ta juya ta ta fita daga office din..tana ganinta a waje ta sauke wani ajiyar zuciya a fili ta furta"kuma Allah ya isana wlh..inyamurin banza"...shi kuwa sai daga baya duk haushin kanshi yabi ya kamashi...wai ma ina ruwanshi da rayuwarta ne at the first place...mamakin kanshi yakeyi shi that ya tsani Fulani especially na Gombe amma wai shine har yake kokarin protecting yarinyar da yasan asalin ‘yar Gombe ce?..baisan ko don sbd mutuncin mahaifinta da yake gani bane...abu guda daya sani shine dukda kasancewar babanta bafulatani kuma na Gombe yana matukar ganin kima da darajarshi and shine mutum na farko daya faraji ya kwanta mishi a rai bayan sanin cewa shi din bafulatanin Gombe ne...kilan sbd kyawawan maganganun da yayi kan Dad dinshi ne amma maganan gaskia mutumin yayi mishi dari bisa dari...itama kuma ‘yar tashi yasan sbd mahaifinta yakejin abunda yakeji and nothing more.
The next day which is Wednesday ranan ne ake inviting mawaqa from different states suzo suyi performing a makarantan...Bobby na kwance tun safe a daki ko parlor ya kasa fitowa...kawai jin jikinshi yakeyi wani iri that har yake tunanin kilan hakura zaiyi da shiga college din nan kawai...dukda yayi mata mgn jiya and yanada tabbacin ta tsorata sai yakejin kaman yayi zamanshi a gida or better still ya tafi Hospital dinshi kawai ba sai yaje ba balle yaga abunda zai 6ata mishi rai...haka yayita kwance a daki bai fito ba saida Mummy ta aiko a kirashi...yana saukowa daga gado ya fada bayi yayi wanka snn ya fito ya shirya kanshi cikin wata armless shirt da wando three qtr snn ya nufi parlor...parlon Mummy ya samesu zaune gaba daya as aunty sumy na gida itama ranan bataje aiki ba Miemie ma bataje sch ba sbd fever data kwana dashi ita kuma ilham tun 1 aka tashesu...karasawa yayi ciki ya zauna da igbo ya gaida Mummy itama ta amsa da igbo snn tayi adding da"yau baka fita ne naga har yanxu baka shirya ba?.."dan ta6e baki yayi yace"i just don’t feel like going out..i think zamana zanyi a gida in huta"...Aunty Sumy tace"aikam bai kamata kaki zuwa ba Bobby..remember it’s a Festival week and abune wanda yake taking place once in a year sai nakega kaman bai dace kaki zuwa ba ko don sbd guests dinku"...Mummy ma na gyada kai tace"sumayya gaskia ta fada Bobby"..shiru yayi cikin ranshi yana ayyana bazaku gane bane...abun kaman hadin baki kawai sukaji sallamr Nur a parlon...Bobby ya kulle ido tareda fadin"the fool is here..nasan yanxu ko banida intention din fita saina fita ko don nacinshi"...daria Mummy sa aunty sumy suka saka jin abunda yace...Nur daya karaso ciki ya zauna ya shiga gaisawa dasu Mummy shima cikin igbo...aunty sumy tace"wlh har mantawa nake Nur yanajin igbo sbd bai cikayi ba unlike abokinshi da mgn daya biyu sai ansa igbo a ciki"...murmushi Nur yayi yana shafa kanshi yace"wlh ni kaina ina manta inajin yaren aunty...gaba daya hausawa sun janyeni"...daria suka sake yi Mummy tana ai dole hausawa su janyeshi tunda yake zaune a kano...bayan sun gama Nur ya juya yana kallon Bobby kafin yayi mgn Bobbyn ya mike yana cewa"ba saika 6ata bakinka ba nasan meya kawoka..ka bani just 5 mins zan shirya in fito"...daria gaba daya suka kara sawa Bobby ya wuce flat dinshi...aunty sumy tace"Nuru kai kadaine maganin Bobby gashi tun kafin kayi mgn an tafi shiryawa"...dariyan shima yasaka yace"kinsanshi baya son naci ai..ni kuma indai inason yayi abu bana barinshi har saina samu abunda nakeso"...bayan 5 mins ya fito a shirye kaman yanda ya fada...Nur na ganinshi ya mike yana sallama dasu Mummy Ilham tace"uncle bobby inaso inje plss"..kallonta bobby yayi sai kuma yace"no kiyi hakuri sai gobe kuje tareda su aunty kinji"..makale shoulder dinta tayi tana fadin"oh oh inaso inje yau"...kallonta kawai yakeyi totally speechless..shi ba son zuwan nan nasu yakeba wlh..ko gobe da aunty sumy tace zasuje suji lecture da za’ayi ba so yakeyi ba...Nur da yaga tana shirin sakin musu kuka yace"zamuje dake baby don’t cry"...nan da nan ta washe bakinta tana tsallen murna..."uncle Nur"..yaji Miemie ta kira sunanshi...a hankali ta juya yana kallonta sai yaga tayi narai narai tana kallonshi...murmushi ya saki dan ya gane mgn take mishi a haka..so take taje itama and tana tsoron furtawa sbd Oga Bobby kada ya hana...saida ya dan saci kallon Bobbyn snn ya dubeta yace"kema zakije kou?.."daga mishi kai tayi da sauri..yace"to je dauko mayafinki"..da sauri ta mike zuwa dakinta ta dakko veil da phone dinta ta fito...Bobby da haushi ya isheshi ya bude baki zai fara masifa Mummy tace"don’t say anything plss..kuje dasu su gani ai ba dadewa zaayi ba"..gum ya maida bakin nashi ya tsuke ba tareda ya fadi abunda yayi niyya ba...sallama sukayi musu suka fita Bobby ya shiga motanshi tareda driver da kuma ilham shi kuma Nur ya dauki Miemie a nashi motan suka tafi.
Tsaye take gaban mirror dinsu tanata kallon kanta kaman bata ta6a ganin mirror ba...straight gown ce a jikinta na wani lace mai kyau..dinkin yabi jikinta ya kwanta luf luf hakan kuma ya baiyanar da beautiful figure dinta...daurin dankwalinta Zara Buhari as usual gashinta ya leko ta karkashin daurin..gaba daya ranta ba dadi duk ma tasan ba jin dadin yau din zatayi ba sbd Bobby..duk ta tuna kashedin da yayi mata jiya na idan tayi wani abu zai hadata da daddy sai taji kaman tasa kuka wlh...yanxu haka yakeso taje tayi zaune a wurin tayita kallonsu knn ita bazatayi rawa ba...da yasan yanda take kaunar rawa da baiyi mata haka ba wlh..kawai rawan yakema bala’i jiya kaman zuwa tayi club ta kwana...Billy ta shigo dakin tana sanye cikin kayanta irin na Aysha sak har dinki da daurin dankwalinsu iri daya...batace mata komai ba ta karasa cikin dakin ta dauko veils dinsu da suke zube kan bed dinta ta hada da wayoyinsu snn taja hannun Aysha suka fita daga dakin...binta kawai takeyi har suka isa compound snn ta saketa ta mika mata veil da wayanta ba musu ta kar6a ta yafa itama Billy ta yafa nata snn tace"nasan in muka daka ta taki zamu iya kwana nan ciki baki gama kallon madubi ba..na fada maki idan kika kiyaye babu abunda ya isa ya maki amma har yanxun kinki kwantar da hankalinki”..juyawa Aysha tayi tana kallonta kaman zatasa kuka tace"yandu fisabilillahi saidai inje inyi zaune kaman gunki ni bazanyi abun arziki ba?..ai wnn rashin imani ne wlh"..ta karasa mgn hawaye na cikowa idonta...daria yaso kufcewa Billy amma ta gimtse suka fita daga wurin...inda Sa’eed ke tsaye suka nufa kafin su karaso ya bude musu mota Aysha ta shiga gaba Billy kuma baya snn shima ya shiga ya tayar da motar suka tafi...a hanya ya dubi bestyn tashi yaga fuskan nan cunkus sai ya kallo Billy ta mirror yace"waya ta6amin besty ta?.."daria Billy ta saki tace"akan mgnr jiya nefa"..dan murmushi shima ya saki yana kokarin controlling dariarshi yace"besty har yanxu mgnr rawan ne dai?.."a fusace ta juya tana kallonshi tace"malam ba ruwanka dani tunda biyewa Billy kake kunamin daria...kawai sai inje inyi zaune ni bazanyi rawa ba sbd rashin imani"...ta karasa mgn hawaye na sake ciko eyes dinta...wnn karon kasa 6oye dariar sukayi dan dagashi har Billyn basu san sanda ta fito ba...daria sukeyi sosai sai kace ta6a66u Aysha kuma ta shaqa iya shaqa kawai sai ta rufe fuska da hands dinta ta wani rushe da matsanancin kuka...ganin kukanda take sai darian ya sake zuwa musu aikam sukaita yinshi knr sabbin kamu saida sukayi me isarsu snn suka bari...Sa’eed ya dan juya yana kallonta with a little smile yace"besty dan Allah kiyi hakuri kinji..nifa bake nakewa daria ba"...yana rufe baki Billy ma tace"nima na ranste ba dake nake ba dan Allah ki bar kuka"...ai kaman ma sunce tacigaba don kara sautin kukan tayi hadda su buga kafafu a kasa ba shiri Sa’eed ya gangara gefen titi yayi parking...juyawa yayi yana kallonta ya wani marairaice yace"yanxu besty dan girman Allah bazakiyi shiru ba?..nace fa am sorry kuma da gaske ni ba dake nake ba"...banza tayi dashi tana cigaba da kukanta...yana mata ciwo idan ta tuna saidai kawai taje wurin a matsayin hoto bazatayi rawa ba...gashi ance hadda favorite mawaqinta aka dauko Ado Gwanja kuma ace bazatayi rawa ba ai wlh an cuceta...wayanta dake ajiye kan dashboard ne ya fara ringing Sa’eed yakai hannu ya dauka ganin yanda tayi banza da wayan...Baby boo ya gani kan screen din dan haka ya juya screen din yana nunawa Billy..da sauri tace"yauwa dauka kace masa yazo ya rarrashi kayarshi tunda mu taki ta sauraremu"...ba musu Sa’eed yayi sliding tareda sawa a speaker...on the other side Prof Ahmad yace"my baby girl"...hada ido Sa’eed sukayi da Billy suna kunshe daria kafin ya maze yana cewa"ahm ba ita bace sunana Sa’eed"...Prof yace"ai besty zaka cemin yanda zanfi ganewa"...Sa’eed ya kara sakin murmushi before yayi adding"besty ce dama tun daxu take kuka wlh kuma munyi iya bakin kokarinmu taki tayi shiru"...hankalinshi har ya fara tashi yace"wait voice dinta ne nakeji tana kuka yanxu?.."da sauri Sa’eed yace"itace wlh...mun rasa yanda zamuyi da ita"...Prof yace"bata waya muyi mgn"...ba musu Sa’eed ya ajiye wayan kan laps dinta...voice dinshi taji yana fadin"hello baby girl"...dan dakatar da kukan tayi tana goge tears dinta tace"umhum"..yace"why are u crying baby girl..waya ta6amin ke?.."saida ta sake goge tawagar hawaye da suka biyo fuskarta tace"ba komai"...yace"no ban yadda ba baby kodai inzo ne?.."girgiza kai tayi tace"aah.."yace"then promise me u will stop crying inba haka ba kuma am coming"...a hankali tace"I promise"...yace"yauwa my little baby girl i love u kinji?..and zanzo da daddare sakin fadamin wanda yasa babyna kuka"...kai take gyadawa kaman yana ganinta kafin tace"toh.."yace"ohk bye"...itama tace"bye.."snn ta ajiye wayar...Billy da Sa’eed hanci da baki suka saki suna kallon ikon Allah ganin har ta dea kukan kaman ba itane suke roki ta dena ba amma taki...bata kalli kowadaga cikinsu ba ta maida kanta jikin window...suma basuce mata komai ba as suna tsoron su sake mgn ta kuma langabe musu Sa’eed ya koma seat dinshi ya zauna snn tada motar suka karasa cikin makarantan.
Wucewa sukazo yi ta daidai inda suke tsaye da alama wani suke jira...Bobby rikeda hannun Ilham Miemie kuma na tsaye kusada Nur don ko kadan batason hada ido da Bobby data tabbatar haushinta yakeji for following them...Bilkisu da Sa’eed ne suka fara tahowa suna zuwa inda suke gaishesu snn suka wuce ita kuma tana baya dan cewa tayi bazata jera dasu ba...ganinshi tsaye a wurin ta sake dinke fuskanta tsaf tana cigaba da tafiya kaman batasan suna wajen ba...kafin ta wuce Nur ya kira sunanta"Lamido"...a hankali ta juya tana kallonshi with a little smile kan face dinta tace"Sir good afternoon"..yace"afternoon ya gajia"...murmushi kawai tayi batace komai ba...Miemie da a kallon farko taji ta burgeta sbd kyanta itama ta gaisheta..Aysha ta amsa ta murmushi tana mamkin inda provost ya samo yarinyar me kyau haka...so tayi ta wuce batareda ta gaishe da Bobby ba amma sai taga bai dace ba kuma yana iya hadata da daddy dan haka ta dan juya tana kallonshi a kaikaice fuskan nan ba fus tace"ina yini"...ko kallon inda take baiyi ba balle ya amsa mata...ita kuma jin yayi shiru ta daga ido sai taga wayanshi ma yake dannawa aikuwa ta daddage ta murguda masa baki sai kuma karaf a idanunshi...idanunta na sauka cikin nashi tayi kasa da nata da sauri...kallonta yayi for like 2 minutes snn ya dauke kai...ita kuma juyawa tayi zata tafi Ilham da har yanxu ke rikeda hannunshi tace"Ehihie Oma"...juyawa Bobby yayi yana kallonta da mamaki jin tayi mata igbo..kafin yayi mgn Aysha data juyo itama tana kallonta with smile tace"hey I don’t understand igbo...how are u"..ilham ta saki murmushi tace"am fine"...Aysha ta gyada kai dan yarinyar sosai ta burgeta sai ta ganta kaman Yusra don itama akwai surutu...tace"ya sunanki?.."da sauri ilham tace"sunana Nadia amma ilham ake cemin..mamana kuma sunanta Sumayya muna cemata aunty...wancan kuma sunan..."bata karasa ba Bobby ya toshe mata baki yana hararanta yace"and who asked u all these?.."turo baki tayi tace"Uncle Bobby let me finishi plss"...bai bari ta sake mgn ba ya kama hannunta suka bar wajen...Aysha ta bisu da kallo tana hararan bayanshi kaman idanun zasu fado...tsaki taja tacigaba da tafia itama...tana shiga inda hall din yake kafin ta karasa Bobby dake tsaye yana jiran shigowanta yace"come here"...juyawa tayi a tsorace tana kallonshi don batasan da mutum ba a wurin...ya wani hade rai yace"bazaki zoba?.."turo baki tayi ta wuce inda yake...tana karasawa ta rungume hanu tana ciccin magani and hakan bai dameshi ba ya nuna gashinta dake a waje fuska babu alamun wasa yace"maida wnn gashin da kika fito dashi"...dagowa tayi ta kalleshi hawaye har sun ciko idonta sbd haushi...har yanxu idan ta tuna batada daman yin rawa a wurin nan sai taji kaman ta shakeshi ya mutu...ganin yana mata wnn kallon da bata so takai hannu ta tura gashin nata ciki...ya bita da wani irin kallon kafin yace"now leave"...ba misu ta juya ta tafi daga wurin hawayen dake cikin idonta na gangarowa kasa...shima ya kama hannun ilham zasu shiga saiga Miemie da Nur sun shigo...Nur ya kalleshi da mamaki yace"wai dama baka shiga ba?..meka tsaya yi a nan toh?.."banza yayi dashi yaja ilham suka shiga ciki...shima shiga cikin sukayi yana mamakin abunda ya tsaidashi a waje bayan tun daxu ya shigo.
0 comments:
Post a Comment